A wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho da takwaransa na Faransa Emmanuel Macron a yammacin jiya Lahadi, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da dabi’ar nuna fuska biyu daga Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya, yana mai cewa irin wannan dabi’a ta nuna fuska biyu za ta janyo rugujewa da haifar da matsaloli da dama ga tsaron yankin da ma duniya baki daya.

A yayin wannan tattaunawa, shugaba Pezeshkian ya ce, wadannan ayyuka na nuna fuska biyu sun haifar da matsaloli da dama ga harkokin tsaro na yanki da na duniya, kuma ana sa ran hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA za ta mutunta haƙƙin kasashe da guje wa ɗabi’a nuna fuska biyu a fagen ayyukanta da kuma kare haƙƙin ƙasashe membobinta.

A martanin da shugaban kasar Faransa ya nuna dangane da matakin Iran na dakatar da hadin gwiwa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, shugaba Pezeshkian ya soki yadda babban sakataren hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA ke bayar da rahotannin da ba su dace ba kan shirin makamashin nukiliyar Iran da kuma rashin yin Allah wadai da harin da aka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, wanda ya saba wa dokokin kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hukumar kula da makamashin nukiliya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jagorantar taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC) a ɗakin taro na Majalisar da ke Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

Kafin a fara taron, Shugaban Ƙasa ya rantsar da Farfesa Dakas James Dakas da Dakta Uchenna Eugene a matsayin Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki ta Ƙasa da Kwamishina.

Majalisar ta kuma dakatar da taron na minti ɗaya domin girmama marigayi Cif Audu Ogbe, wanda ya kasance memba a majalisar a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Shehu Shagari, haka kuma a ƙarƙashin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Cif Ogbe ya rasu a ranar Asabar, 9 ga watan Agusta, yana da shekaru 78.

 

Daga Bello Wakili

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
  • Hukuma Mai Kula Da Sauka Da Tashin Jiragen Sama A Paris Ya Dakatar Da Wani Ma’aikacinta
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Iran Tace Ma’aikatar Harkokin Waje Kasarce Take Kula Da Lamuran Makamacin Nukliyar Kasar
  • Armenia Ta Tabbatarwa Iran Zata Kula Da Muradunta Bayan Yarjeniya Da Azarbaijan A Amurka
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa