Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
Published: 30th, June 2025 GMT
A wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho da takwaransa na Faransa Emmanuel Macron a yammacin jiya Lahadi, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da dabi’ar nuna fuska biyu daga Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya, yana mai cewa irin wannan dabi’a ta nuna fuska biyu za ta janyo rugujewa da haifar da matsaloli da dama ga tsaron yankin da ma duniya baki daya.
A yayin wannan tattaunawa, shugaba Pezeshkian ya ce, wadannan ayyuka na nuna fuska biyu sun haifar da matsaloli da dama ga harkokin tsaro na yanki da na duniya, kuma ana sa ran hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA za ta mutunta haƙƙin kasashe da guje wa ɗabi’a nuna fuska biyu a fagen ayyukanta da kuma kare haƙƙin ƙasashe membobinta.
A martanin da shugaban kasar Faransa ya nuna dangane da matakin Iran na dakatar da hadin gwiwa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, shugaba Pezeshkian ya soki yadda babban sakataren hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA ke bayar da rahotannin da ba su dace ba kan shirin makamashin nukiliyar Iran da kuma rashin yin Allah wadai da harin da aka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, wanda ya saba wa dokokin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hukumar kula da makamashin nukiliya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF
Wani sabon rahoto da Asusun Bayar da Lamuni IMF ya fitar ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.
IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.
Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Aminu Ɗantata a KanoJaridar Cable ta ruwaito cewa, Nijeriya tana mataki na 12 a cikin kasashe mafiya talauci bisa la’akari da karfin tattalin arziki a ma’aunin GDP na Dalar Amurka 807 a bana.
Kawo yanzu dai shekaru biyu bayan kaddamar da jerin sauye-sauye ga tattalin arziki, amma daga dukkan alamu Nijerya na dada fadawa cikin matsalar talauci idan aka yi la’akari da kasashe 189 da IMF ya gudanar da bincike a cikinsu.
A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Najeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.
Ana kallon sabon rahoton a matsayin alamun kasawa a bangare na masu mulkin Nijeriya da ke fadin cewar suna da burin ceto kasar da ke kara samun nakasu, kamar yadda Ibrahim Shehu, sakataren kungiyar inganta tattalin arzikin arewacin Najeriya ya bayyana.
Akalla Naira tiriliyan 21 ne ake jin matakan gwamnatin kasar guda uku sun samu daga zare tallafin man fetur a shekaru guda biyu.
Ko bayan wasu Naira Tiriliyan 96 da masu mulkin na Abuja suka karba da sunan bashi, akwai Naira tiriliyan guda a shekara da masu mulkin ke samu sakamakon ragin tallafi bisa kudin wuta.