Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
Published: 29th, June 2025 GMT
Hasarar da gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi a hare-haren da ta kai wa kasar Iran ya kai dala biliyan uku
Kafar watsa labaran Bloomberg ta Amurka ta yi kiyasin cewa: Hasarar da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi a yakin da ta yi da Iran ya kai kusan dala biliyan 3, saboda gyaran gine-gine da suka lalace da kuma biyan diyya ga kamfanoni.
Kafar ta Bloomberg ta bayyana a cikin wani rahoto cewa: Hasarar da gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi na nuni da irin yadda Iran ta kutsa kai cikin tsaron Isra’ila a cikin kimanin makonni biyu da harba makaman masu linzami kan yankunan kasar.
Jaridar Amurka ta rawaito wani jami’in gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila yana cewa: “Wannan shi ne kalubale mafi girma da suka fuskanta, wanda ba a taba samun irin wannan barna a tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba.”
Bayanai na hukuma da ma’aikatar kudi ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta fitar a cikin wannan yanayi na nuni da cewa: Irin barnar da aka yi na nuna irin yadda makamai masu linzami na Iran suka kutsa cikin tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila a cikin kimanin makonni biyu da harba makaman.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: haramtacciyar kasar Isra ila Isra ila ta yi
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter A Kasar Habasha
An yi girgizar kasa mai karfin daraja 5.7 a ma’aunin Richter a kasar Habasha a jiya Asabar.
Cibiyar dake kula da ilimin kasa ta kasar Jamus ta bayyana cewa, an yi girgizar kasar ne da zurfin kilo mita 10 a karkashin kasa.
Girgizar kasar ta Jiya dai tana cikin jerin girgizar da aka yi ne a cikin kasar ta Habasha a lokuta mabanbanta a wannan shekarar. Sai dai kuma a wannan loakcin ana tsoron cewa za a iya fuskantar aman duwatsu a cikin yankunan da girgizar kasar ta afku.
Daga farkon wannan shekarar zuwa yanzu an yi girgizar kasa har sau 29 a cikin kasar ta Habasha, da karfin wasu daga cikinsu ya wuce daraja 5.
A ranar 3 ga watan Janairu an yi girgizar kasa har sau 11 a rana daya sannan kuma dutsen Dopin ya yi aman wuta.
Yankin Fantali na kasar Habasha yana cikin wuraren su ka fi fuskantar aman duwatsu a tarihin kasar. A 1820 an yi wasu jerin girgizar kasa wanda ya aman wuta ya biyo baya.
A halin yanzu dai hukumomin dake kula da kasa, suna ci gaba da sa ido akan abubuwan da suke faruwa tare da yin gagradin ga mazauna yanki da su kasance cikin fadaka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci