Wani mummunan hatsari ya afku a Masar inda ‘yan mata 18 suka mutu sakamakon fashewar wata motar dakon mai

Wani mummunan hatsarin mota ya afku a kasar Masar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar wasu mata 18 da direban bas a kan hanyarsu ta zuwa gonar inabin domin girbin inabin.

Hatsarin ya afku ne a ranar Juma’a a kan hanyar yankin da ke gundumar Menoufia, bayan wata babbar mota ta yi karo da motar bas din da ke dauke da ‘yan matan 18.

Dukkansu sun fito ne daga kauye daya, Kafr El-Sanabseh, a gundumar Menoufia, kuma dukkansu ‘yan kasa da shekara 21 ne.

Hotunan wannan mummunan hatsarin da aka yi ta yawo da su a shafukan sada zumunta, sun nuna yadda motar bas din ta lalace gaba daya. Hotunan akwatunan gawarwakin ‘yan matan da aka jera su sun haifar da bakin ciki sosa a tsakanin al’umma.

Jami’an tsaro sun cafke direban babbar motar da ke da alhakin hatsarin bayan ya arce daga wurin. An mika shi ga ofishin gabatar da kara na gwamnati, wanda ke gudanar da bincike.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Rikicin filin gona ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu biyu a ƙaramar hukumar Gulani da ke Jihar Yobe. Lamarin ya faru ne a daren Asabar bayan ce-ce-ku-ce tsakanin mazauna ƙauyukan Zango da Azere, waɗanda ke tsakanin iyakokin Gujba da Gulani.

Kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya bayyana cewa shalƙwatar ƴansanda ta Bara ta samu kiran gaggawa daga shugaban ƙauyen Zango a ranar 9 ga Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na dare, inda ya sanar da cewa wasu ƴan daba daga ƙauyen Azere sun kai mummunan farmaki kan manoma.

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah Afam Osigwe Ya Zama Sabon Shugaban Kungiyar Lauyoyi Ta Kasa

Wanda aka kashe sun haɗa da Sani Makeri, mai shekara 40, da Abdullahi Maicitta, mai shekara 35, dukkansu ƴan asalin Zango. An garzaya da waɗanda suka jikkata an kai su zuwa babban asibitin Damaturu domin samun kulawa.

SP Dungus ya ce rikicin ya samo asali ne tun bara lokacin damina, duk da ƙoƙarin hukumar ƴansanda wajen sulhu ta hanyar kwamitin daidaita iyakoki na Jiha. Kwamishinan ƴansandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya la’anci harin tare da bayar da tabbacin cafke masu laifi, kana ya ja hankalin manoma su guji ɗaukar doka a hannu su kuma nemi sulhu ta hanyar hukumomi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama basarake kan zargin yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Gombe
  • Masar ta yi gargadin cewa a shirye take ta dauki duk wani mataki na kare muradunta
  • Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 
  • Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista
  • Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya
  • Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
  • Ana Neman Daukar Karin Matakin Kawar Da Shingayen Dake Hana ‘Ya’ya Mata Zuwa Makaranta A Zamfara
  • Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
  • An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata