Mummunan Hatsari Ya Lashe Rayukan ‘Yan Mata 18 A Kasar Masar Dukkaninsu ‘Yan Kasa DA Shekara 21
Published: 28th, June 2025 GMT
Wani mummunan hatsari ya afku a Masar inda ‘yan mata 18 suka mutu sakamakon fashewar wata motar dakon mai
Wani mummunan hatsarin mota ya afku a kasar Masar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar wasu mata 18 da direban bas a kan hanyarsu ta zuwa gonar inabin domin girbin inabin.
Hatsarin ya afku ne a ranar Juma’a a kan hanyar yankin da ke gundumar Menoufia, bayan wata babbar mota ta yi karo da motar bas din da ke dauke da ‘yan matan 18.
Hotunan wannan mummunan hatsarin da aka yi ta yawo da su a shafukan sada zumunta, sun nuna yadda motar bas din ta lalace gaba daya. Hotunan akwatunan gawarwakin ‘yan matan da aka jera su sun haifar da bakin ciki sosa a tsakanin al’umma.
Jami’an tsaro sun cafke direban babbar motar da ke da alhakin hatsarin bayan ya arce daga wurin. An mika shi ga ofishin gabatar da kara na gwamnati, wanda ke gudanar da bincike.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
Rundunar ’yan sandan Jihar Anambra ta gano gawar wasu mata uku ’yan ƙasar Kamaru da ake zargin waɗanda suka yi garkuwa da su domin neman kuɗin fansa sun kashe su.
Haka kuma, rundunar ta ce ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a lamarin, Nonso Augustine Akpeh da Kingsley Akpeh, waɗanda ake zargin suna cikin gungun masu garkuwar da suka sace matan.
Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADCTun dai a ranar Litinin, 10 ga watan Nuwamban nan ne aka sace matan a garin Anam da ke Jihar Anambra, inda suka saba zuwa sayen kayayyakin kasuwanci.
Jami’an rundunar na sashen yaki da masu garkuwa da mutane da ke Awkuzu ne suka kai wani farmaki, inda aka yi musayar wuta tsakaninsu da masu garkuwar.
A yayin bincike, an gano makamai iri-iri, ciki har da bindiga mai sarrafa kanta da bindigogi ƙirar hannu da kuma harsasai.
Kakakin rundunar, SP Tochukwu Ikenga, ya shaida wa Aminiya cewa dangin matan ne suka kai rahoton bacewar su tun a ranar 13 ga Nuwamba, bayan sun gaza komawa gida daga kasuwar Anam, inda suka saba zuwa.
SP Ikenga ya ce masu garkuwa sun fara neman kuɗin fansa har Naira miliyan 50, amma bayan an yi ciniki suka amince a biya Naira miliyan 2.9.
Sai dai a cewar SP Ikenga, masu garkuwar sun kashe matan duk da ’yan uwan waɗanda abin ya shafa sun biya kuɗin fansar.
A cewar SP Ikenga, wani cikin waɗanda ake zargin ne ya jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa dajin da ake ɓoye waɗanda aka sace, inda a can ne aka gano wurin da ake jefar da gawawwakin nasu.
A yayin binciken ne ɗaya daga cikin ababen zargin ya yi yunƙurin tserewa, amma jami’an suka sake cafke shi.
Mazauna yankin da ke kusa da dajin sun tabbatar wa ’yan sanda cewa wurin ya shahara wajen jefar da gawar mutanen da masu garkuwa da mutane ke kashewa.
Rundunar ’yan sandan ta ce bincike zai ci gaba da gudana, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala.