Baltasar Engonga Ebang, mutumin nan dan kasar Equatorial Guinea da a bara ya saki bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 na fuskantar shari’a a kotu kan badakalar kudade.

Baltasar, wanda tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Rashawa ta kasar Equatorial Guinea ne dai an gurfanar da shi a gaban kotu ne bisa zargin karkatar da kudade a karkashin Ma’aikatar Kudin kasar.

Masu shigar da kara na neman a yanke masa hukuncin daurin shekara 18 a kurkuru sannan a umarce shi ya dawo da wasu kudaden masu yawa.

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota

Ana dai zarginsa ne da almundahana, azurta kai da kuma rub-da-ciki a kan dukiyar al’umma lokacin da yake rike da mukamin hukumar.

Lauyoyi masu shigar da kara na zargin Baltasar da yin babakere a kan kudi har sama da CFA biliyan daya, kwatankwacin sama da Naira biliyan biyu da rabi.

Bugu da kari, lauyoyin na kuma son a yanke masa hukuncin shekara takwas kan laifin almundahana, shekara hudu da wata biyar kan laifin azurta kai, sai kuma shekara shida kan laifin cin amanar ofishinsa.

Lauyoyin sun kuma bukaci kotun ta ci Baltasar tarar CFA miliyan 910 sannan a haramta masa rike kowanne irin ofishin gwamanti na tsawon lokacin da zai shafe a dauren.

To sai dai lauyoyin wanda ake karar sun yi fatali da dukkan laifukan da ake zargin wanda suke karewa da aikatawa da ma sauran wadanda ake zargin, inda suka ce bas u da tushe.

A watan Disambar bara ne dai bidiyoyin Baltasar na lalata da mata sama da 400 suka cika shafukan sada zumunta. Daga cikin matan da aka gan shi yana lalata da su har da matan ministotin kasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Baltasar

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun kafin sanar da sabuwar ƙawance da suka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yi wa wannan haɗaka zagon ƙasa da kawo cikas ga tafiyar.

Ɗaya daga cikin irin waɗannan zagon ƙasa da ake zargin wasu da yi wa wannan sabuwar haɗaka, ita ce na sanar da su rashin samun ɗakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci ƙalilan gabanin taron.

NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan noyayyun ƙalubalen da sabon haɗakar jam’iyyar ADC za ta iya fuskanta gabanin 2027.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa ‘Yan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Fitar Da Rahoton Wadanda Suke Taimakawa Yahudawan Sahayoniyya Wajen Murkushe Falasdinawa
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
  • Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki
  • Kotu A Kasar Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Ayatullahi Baqir Sadr
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
  • Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli