HausaTv:
2025-08-14@13:53:51 GMT

 HKI:Har Yanzu Matatar Man Fetur Ta Haifa Ba Ta Koma Aiki Ba

Published: 30th, June 2025 GMT

 Majiyar ‘yan sahayoniya ta ce, sai zuwa watan Oktoba ne za a iya kawo karshen lalacewar da matatar man fetur din Haifa ta yi sanadiyyar harin makami mai linzami na Iran.

Jaridar “Time Of Isra’il” ta bayyana cewa a tsawon yakin kwanaki 12, Iran ta yi wa Isra’ila mummunan harin mai ciwo da sai yanzu ne sannu a hankali zurfinsa yake bayyana.

A jiya Lahadi ne matatar man fetur ta Haifa ta sanar da cewa; Wani karamin sashe nata ne zai fara aiki, saboda hare-haren makamai masu linzami na Iran.

 Matatar man fetur din wacce ake kira da sunan : “BAZAN” ta ce sai zuwa wata Oktoba ne ake sa ran cewa za ta koma aiki baki daya.

A ranar 15 ga watan Yuni ne dai aikin matatar ya tsaya saboda hare-haren ramuwar gayya da Iran din ta kai, bayan da ‘yan sahayoniyar bisa cikakken goyon bayan Amurka su ka kawo wa Iran hari.

Ita dai wannan matatar man fetur din tana samarwa da HKI man fetur da ya kai kaso 59% da kuma Gas da ake amfani da shi a gidaje da ya kai kaso 52%.

A yayin harin, kamfani da yake tafiyar da matata ya sanar da halakar ‘yan sahayoniya 3.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda ɗaukar matasan da aka horar ƙarƙashin shirin GOSTEC aiki a matsayin cikakkun ma’aikata.

Ya ce wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnati wajen taimaka wa matasa domin rage zaman banza da kuma ba su damar dogaro da kai.

Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan Gwamnatin Gombe za ta ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13

Ya ƙara da cewa, yanzu wasu daga cikin matasan sun za su hidimata wa al’umma, saɓanin halin da suke ciki a baya.

Ya roƙi matasan su zama masu gaskiya, riƙon amana da kishin ƙasa, inda ya bayyana cewa su ne ginshiƙin ci gaban kowace al’umma.

Ɗaya daga cikin matasan da aka ɗauka aikin, Musa Abdullahi, ya ce shirin GOSTEC, ya sauya rayuwarsa daga neman aiki zuwa taimakawa wajen bunkasa tattalin arziƙin jihar.

Ita ma, Fatima Mohammed, ta bayyana farin cikinta da samun aikin gwamnati bayan samun horo a fannin shafukan Intanet, tare da yaba wa gwamnati saboda ƙoƙarin inganta rayuwar matasa.

Bikin, ya samu halartar jami’an gwamnati, ƙungiyoyin matasa, inda aka tattauna kan makomar matasa, ilimi da ci gaban tattalin arziƙi a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe
  • Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya
  • Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
  • Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita
  • Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.