HausaTv:
2025-06-30@10:56:56 GMT

 HKI:Har Yanzu Matatar Man Fetur Ta Haifa Ba Ta Koma Aiki Ba

Published: 30th, June 2025 GMT

 Majiyar ‘yan sahayoniya ta ce, sai zuwa watan Oktoba ne za a iya kawo karshen lalacewar da matatar man fetur din Haifa ta yi sanadiyyar harin makami mai linzami na Iran.

Jaridar “Time Of Isra’il” ta bayyana cewa a tsawon yakin kwanaki 12, Iran ta yi wa Isra’ila mummunan harin mai ciwo da sai yanzu ne sannu a hankali zurfinsa yake bayyana.

A jiya Lahadi ne matatar man fetur ta Haifa ta sanar da cewa; Wani karamin sashe nata ne zai fara aiki, saboda hare-haren makamai masu linzami na Iran.

 Matatar man fetur din wacce ake kira da sunan : “BAZAN” ta ce sai zuwa wata Oktoba ne ake sa ran cewa za ta koma aiki baki daya.

A ranar 15 ga watan Yuni ne dai aikin matatar ya tsaya saboda hare-haren ramuwar gayya da Iran din ta kai, bayan da ‘yan sahayoniyar bisa cikakken goyon bayan Amurka su ka kawo wa Iran hari.

Ita dai wannan matatar man fetur din tana samarwa da HKI man fetur da ya kai kaso 59% da kuma Gas da ake amfani da shi a gidaje da ya kai kaso 52%.

A yayin harin, kamfani da yake tafiyar da matata ya sanar da halakar ‘yan sahayoniya 3.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Filato ba ta aiko da wani wakili zuwa Zariya domin yi wa iyalan waɗanda aka kashe a Ƙaramar Hukumar Mangu a Jihar Filato, ta’aziyya ba.

Aminiya ta ruwaito, yadda wasu matasa suka farmaki motar wasu ’yan ɗaurin aure su 31, inda suka kashe 13 daga cikinsu.

Aminu Ɗantata: Na roƙi Allah kada Ya ba ni abin da mutane ba za su amfana ba Za a yi wa Aminu Ɗantata Salatul Ga’ib a Kano

Sarkin ya bayyana hakan ne lokacin da jagoran shugabannin addinai, Tsohon Ministan Matasa da Wasanni Solomon Dalung, ya jagoranci wata tawaga zuwa fadarsa domin yin ta’aziyya.

Sarkin ya gode wa tawagar bisa wannan ziyara, amma ya nuna damuwa cewa babu ko ɗaya daga cikin wakilan Gwamnatin Filato da ya zo domin yin ta’aziyya ko duba halin da iyalan mamatan ke ciki.

Ya roƙi Gwamnatin Filato da ta ɗauki matakin gaggawa, kuma a tabbatar da adalci.

Haka kuma, ya jaddada buƙatar haɗin kai a tsakanin al’ummar Arewacin Najeriya bai ɗaya, tare da kiran shugabanni su haɗa kai domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Solomon Dalung, ya ce sun zo domin yi wa al’ummar da abin ya shafa da kuma masarautar Zazzau ta’aziyya.

Ya nemi a kwantar da hankali, sannan ya buƙaci gwamnati ta hukunta masu laifin.

Fasto Yohanna Buru, ɗaya daga cikin tawagar, ya bayyana harin a matsayin abin kunya.

Ya kuma ce ya zama dole a cafke masu hannu a harin.

Tawagar ta kuma kai ziyara ga Farfesa Ango Abdullahi kafin su gana da Sarkin Zazzau.

Fasto George T. John, wani daga cikin tawagar, ya ce al’ummar da abin ya shafa na cikin baƙin ciki sosai.

Ya yi Allah-wadai da harin, yana mai cewa hakan mummunan laifi ne.

Yakubu Yusuf, ɗaya daga cikin ’yan uwan waɗanda aka kashe daga Angwan Dantsoho a Ƙaramar Hukumar Kudan, ya gode wa baƙin.

Ya kuma roƙi gwamnatin jihar da ta Tarayya da su taimaka wa marayu da mamatan suka bari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
  • Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
  • Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
  • Monaco ta dauki Paul Pogba
  •  Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
  • Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 
  • Aminu Ɗantata: Na roƙi Allah kada Ya ba ni abin da mutane ba za su amfana ba
  • Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike