Aminiya:
2025-06-29@13:11:35 GMT

Har yanzu mun gaza gano dalilin ɓullar COVID-19 — WHO

Published: 29th, June 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta yi duk mai yiwuwa domin bankaɗo tushen ɓullar cutar coronavirus da kuma dalilin fantsamarta a sassan duniya.

Shugaban hukumar, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana hakan yana cewa duk da faɗi-tashin ƙwararru, har yanzu ba su da wani cikakken bayani kan abin da ya hana su cimma buri kan binciken da suke gudanarwa.

Cutar Coronavirus na cikin cutukan da suka fi gigitar da duniya, wadda ba za’a taɓa mantawa da ita a duniya ba, la’akari da yadda ta yi sanadin mutuwar miliyoyin mutane, da kuma tilasta sanya dokar hana shige da fice, matakin da ya tsayar da duniya cak.

An dai fara samun ɓullar cutar a yankin Wuhan na ƙasar China a ƙarshen shekarar 2019, duk da dai ƙasar ta musanta hannu a ɓarkewar cutar.

A 2021 ne Tedros ya ƙaddamar da wani kwamitin ƙwarraru kan kimiyya don su gudanar da bincike kan yadda cutar ta samo asali da kuma yadda cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ta fantsama ko ina a duniya.

Sai dai ya ce duk da wasu kwamitocin da aka kafa bayan wannan aka kuma dora musu alhaki iri ɗaya amma har yanzu an gaza gano ko da dalilin ɗaya gamsashe abin da ke zama tamkar almara.

A cewarsa, abinda aka iya ganowa da kuma tabbatarwa kawai shi ne cewa cutar ta tsallaka jikin ɗan adam ne daga wasu dabbobi, amma babu tabbacin waɗanne nau’in dabbobi ne kai tsaye.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City

Tsohon tauraron ƙungiyoyin Manchester United da Real Madrid, Ruud van Nistelrooy ya ajiye aikinsa na horas da Leicester City bisa fahimtar juna.

Wannan na zuwa ne bayan da a ƙarƙashin jagorancinsa ƙungiyar ta yi wasanni 27 da ta gaza taɓuka abin a zo a gani a cikinsu, lamarin da ya kai ta ga faɗawa gasa mai daraja ta biyu a Ingila wato Championship.

Wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta ce an cimma matsaya tsakaninta da Van Nistelroy ne bayan tattaunawar da suka yi.

A ƙarshen watan Nuwamban da ya gabata, bayan da ta kori Steve Cooper a lokacin da suke matsayi na 16 a gasar Firimiyar bara, Liecester City ta ƙulla yarjejeniya da Van Nistelrooy, kwangilar da ba za ta ƙare ba sai a shekarar 2027.

To amma duk da sauyin da aka samu kwalliya ta gaza biyan kuɗin sabulu domin kuwa a haka suka yi ta tafiya da ƙyar.

Daga ƙarshe ma dai ƙungiyar ta sha kashi da ci 1-0 a karawar ta Liverpool a ranar 20 ga watan Afrilu, rashin nasarar da ta tabbatar da cewar ƙungiyar ta yi adabo da gasar Firimiya sai kuma wani jiƙon.

A halin yanzu dai ana sa ran tsohon Kocin Burnley da Everton, Sean Dyche ya maye gurbin da Nistelrooy ya bari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
  • Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
  • Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
  • Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 
  • Aminu Ɗantata: Na roƙi Allah kada Ya ba ni abin da mutane ba za su amfana ba
  • Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya
  • Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada