Aminiya:
2025-08-13@19:20:47 GMT

Har yanzu mun gaza gano dalilin ɓullar COVID-19 — WHO

Published: 29th, June 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta yi duk mai yiwuwa domin bankaɗo tushen ɓullar cutar coronavirus da kuma dalilin fantsamarta a sassan duniya.

Shugaban hukumar, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana hakan yana cewa duk da faɗi-tashin ƙwararru, har yanzu ba su da wani cikakken bayani kan abin da ya hana su cimma buri kan binciken da suke gudanarwa.

Cutar Coronavirus na cikin cutukan da suka fi gigitar da duniya, wadda ba za’a taɓa mantawa da ita a duniya ba, la’akari da yadda ta yi sanadin mutuwar miliyoyin mutane, da kuma tilasta sanya dokar hana shige da fice, matakin da ya tsayar da duniya cak.

An dai fara samun ɓullar cutar a yankin Wuhan na ƙasar China a ƙarshen shekarar 2019, duk da dai ƙasar ta musanta hannu a ɓarkewar cutar.

A 2021 ne Tedros ya ƙaddamar da wani kwamitin ƙwarraru kan kimiyya don su gudanar da bincike kan yadda cutar ta samo asali da kuma yadda cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ta fantsama ko ina a duniya.

Sai dai ya ce duk da wasu kwamitocin da aka kafa bayan wannan aka kuma dora musu alhaki iri ɗaya amma har yanzu an gaza gano ko da dalilin ɗaya gamsashe abin da ke zama tamkar almara.

A cewarsa, abinda aka iya ganowa da kuma tabbatarwa kawai shi ne cewa cutar ta tsallaka jikin ɗan adam ne daga wasu dabbobi, amma babu tabbacin waɗanne nau’in dabbobi ne kai tsaye.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Damina lokaci ne da ɗan Adam yake matuƙar bukata. Da za ta yi jinkiri, sai a ga hankalin kowa ya tashi.

A lokaci guda kuma, yadda damina kan hana wasu harkoki gudana kan jefa wasu mutane cikin wani irin yanayi.

NAJERIYA A YAU: Shekara nawa shugabanni ke bukata don cika alkawuran zabe? DAGA LARABA: Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani?

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan yadda damina kan shafi rayuwar ƙananan ’yan kasuwa da masu ƙananan sana’oi.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe
  • Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno
  • Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
  • Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
  • Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i
  • Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza
  • Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam