Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Al’ummar Iran masu juriya za su tsaya tsayin daka har zuwa digon jini na karshe

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Al’ummar Iran masu juriya za su tsaya tsayin daka har zuwa digon jini na karshe a kan duk wanda ya nemi juya akalarsu.

Araqchi ya rubuta a cikin shafinsa na yanar gizo a dandalin sada zumunta na X cewa: “Har yanzu, al’ummar Iran masu girma sun nuna wa duniya karfinsu da juriyarsu.”

Ya kara da cewa: Karfin kadawar guguwar masu kishin kasa da suka fito kan tituna domin karrama shuwagabannin soji da suka yi shahada, malamai, masu bincike, da ‘yan kasa, ciki har da mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da matsoratan ‘yan sahayoniyya suka yi wa kisan gilla, dukkansu suna dauke da sako karara.

Araqchi ya ci gaba da cewa: Sabanin gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu Rauni, marasa karfi, Iraniyawa ba su taba boye hasarar da aka yi musu. Suna alfahari da shahidansu, su ne abin koyinsu. Ku tabbatar cewa, kowane jami’i ko masanin kimiyya da Iran ta rasa, akwai ɗaruruwan da suke layi don maye gurbinsu.

Ya jaddada cewa: Al’ummar Iran masu karfi da juriya za su tsaya tsayin daka har sai digon jini na karshe a kan duk wanda ke son yanke hukunci kan makomarsu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Al ummar Iran masu

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Masana Iran da suka yi shahada a lokacin yaki babu laifin da suka aikata ban da hidima ga al’ummarsu

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi kakkausar suka kan shirun da masu da’awar kare hakkin bil’adama da zaman lafiya da tsaro suka yi dangane da laifukan gwamnatin ‘yan sahayoniyya, yana mai cewa: Masana kimiyyar Iran da suka yi shahada ba su aikata komai ba face hidimar al’ummar Iran a fadin duniya, amma gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kashe su.

Masoud Pezeshkian ya halarci bikin karrama masana kimiyya da suka yi shahada a tsangayar koyar da fasahar nukiliya ta jami’ar Shahid Beheshti a safiyar ranar Talata, inda ya jinjinawa hotunan malaman kimiyya da suka yi shahada a cikin jami’ar tare da sanya hannu kan littafin bakin da suka halarta.

Pezeshkian ya kara da cewa: “Shi da kansa ya yi hulda da wadannan masoya saboda matsayinsu da kuma nauyin da ke wuyansu, ba su aikata wani laifi ba face sani da kuma iya yanke shawarar samarwa kasarsu fasahar zamani.”

Shugaban ya soki lamirin masu ikirarin kare dimokuradiyya, ‘yancin dan Adam, zaman lafiya da tsaro, yana mai cewa: “Wannan da’awar ba komai ba ce illa karya, wadanda aka rataye hotunansu a nan ba su yi komai ba illa hidimar al’ummar Iran da kokarin kare kasar daga cin zarafi na zalunci a duniya, amma gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kashe su.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe August 13, 2025 Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Jaddada Kasancewar Iran Tare Da Kasar Lebanon Koda Yaushe August 13, 2025 Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin August 13, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida  August 13, 2025 Wakilan Hamas sun isa Alkahira don shawarwarin tsagaita wuta a Gaza August 13, 2025 Iran: Amurka Da Isra’ila Ne Da Kansu Suka Bukaci Dakatar Da Bude Wuta August 13, 2025 Habasha: Madatsar ruwanmu amfanin dukkanin kasashen yankin ne August 13, 2025 Bankin Duniya Zai Kashe $300m Don Inganta Rayuwar ’Yan Gudun Hijira A Arewacin Nijeriya August 13, 2025 Nijeriya Da Isra’ila Na Kara Karfafa Alaka A Tsakaninsu August 13, 2025 Kasashe 27 Sun Bukaci Isara’ila Ta Kawo Karshen Hana Shigar Da Abinci A Gaza August 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Furucin Netanyahu Game Da Kafa “Babbar Kasar Isra’ila’
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy
  • Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Iran Tace Ma’aikatar Harkokin Waje Kasarce Take Kula Da Lamuran Makamacin Nukliyar Kasar
  • Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro