Aminiya:
2025-10-13@17:54:16 GMT

Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu

Published: 2nd, July 2025 GMT

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Garba Shehu, ya ce sam maigidan nasa bai yi wani abu don yi wa yunƙurin Bola Tinubu na zama Shugaban Najeriya a 2023 zagon ƙasa ba.

Ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Talata yayin wani taron manema labarai gabanin kaddamar da sabon littafin da ya rubuta a kan zamansa mai magana da yawun Buhari, wanda za a kaddamar ranar tara ga watan Yuli.

’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

An dai yi zargin cewa da gangan Buhari ya jinkirta cire tallafin man fetur har zuwa karshen mulkinsa a 2023 domin ya hada ’yan Najeriya fada da Tinubu.

Kazalika, ’yan Najeriya sun rika sukar lamirin gwamnatin Tinubu kan kawo wahalhalu da yunwa tun bayan sanar da cire tallafin man da shugaban ya yi ranar da aka rantsar da shi.

To sai dai Garba Shehu ya karyata batun cewa an shirya cire tallafin ne saboda a yi wa Tinubu zagon kasa.

Kakakin ya ce ya cika da mamakin labarin, yana mai cewa ba yadda za a yi Buhari ya yi hakan ga dan jam’iyyarsa, tamkar daga wata jam’iyyar zai karbi mulkin daga hannunsa.

Ya ce, “Da Buhari da Tinubu duk ’yan APC ne, saboda haka ban ga ta yadda za mu shirya abin da zai yi wa gwamnatinmu zagon kasa ba.

“Buhari mutum ne da ya tsani harkar rashawa, ya shigo gwamnati da gaskiyar shi, kuma har ya gama a haka yake. Ya yi iya bakin kokarinsa ga ’yan Najeriya kuma tarihi ba zai manta da shi ba. shi ba mutum ba ne mai kwarmato, aiki kawai ya yi,” in ji Garba Shehu.

Ya kuma ce shi a karan kansa bai yi laifi ba saboda ya kyale tsohon maigidansa kuma tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya yi aiki a gwamnatin Buhari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari Garba Shehu Garba Shehu

এছাড়াও পড়ুন:

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Ta ce, “Dole ne akwai kalubale da dama, wanda daga cikinmu muke fuskanta a yayin shigowa wannan masana’anta, amma dai ni babu wani abu da zan iya tunawa, illa wani wanda na iske a masana’antar ya karbi zunzurutun kudi har Naira 50,000 a mabanbantan lokuta da sunan zai yi min rijista a masana’antar, kuma bai yi ba, daga karshe ma na gano cewa; kudin rijistar duka-duka Naira 5,000 ne.

 

A wata hira da Khadija ta yi da gidan Rediyon Hikima, ta bayyana cewa, matukar ta samu abin da ya kawo ta masana’antar (Kudi), to nan da shekara daya ma; za ta iya shiga daga ciki, ma’ana za ta samu miji ta yi aurenta na Sunna.

 

Khadija, wadda ta ce; ita haifaffiyar birnin Maiduguri ce ta Jihar Borno, wadda zama ya dawo da ita birnin Kanon Dabo, ta kuma bukaci masu kallon su da su dinga nuna musu soyayya kamar yadda suke nuna wa sauran jaruman duniya, musamman wadanda ke cikin masana’antar Bollywood ta Kasar Indiya.

 

“Akwai bukatar dukkaninmu, mu hada karfi da karfe don ganin mun taimaki junanmu, ba mu koma gefe muna zagin junanmu ba, abin da ya sa na fadi haka kuwa shi ne, akwai lokacin da wani ya zo neman aurena, amma wasu suka zagaya baya suka hure masa kunne a kan cewa; kada ya sake ya aure ni, saboda ni jarumar fim ce. Ta kara da cewa; mu ma Hausawa ne kamar mafi yawan masu kallonmu, sannan kuma bai kamata ku yi la’akari da duk wani abu da kuka gani a cikin fim, wajen yanke hukuncin cewa, halin dan fim kenan ko a zahiri ba.

 

Daga karshe, Khdadija ta ce; “Dukkanninmu ‘yan fim, muna kokari wajen ganin mun killace kanmu( Sirrinta al’amuranmu), domin kauce wa zargi, duk wani wanda ka ga yana fallasa halayensa na zahiri a shafukansa na sada zumunta, to ba dan fim ba ne, kawai yana zuwa neman taimako wajen masu shirya fina-finai ne su saka shi ya fito sau biyu ko sau uku a fim, domin su samu na cefane, amma ba lallai ne ya zama cikakaken dan fim ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Nishadi Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri? October 11, 2025 Nishadi Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano October 6, 2025 Nishadi An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana October 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya