Aminiya:
2025-07-03@00:58:09 GMT

Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu

Published: 2nd, July 2025 GMT

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Garba Shehu, ya ce sam maigidan nasa bai yi wani abu don yi wa yunƙurin Bola Tinubu na zama Shugaban Najeriya a 2023 zagon ƙasa ba.

Ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Talata yayin wani taron manema labarai gabanin kaddamar da sabon littafin da ya rubuta a kan zamansa mai magana da yawun Buhari, wanda za a kaddamar ranar tara ga watan Yuli.

’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

An dai yi zargin cewa da gangan Buhari ya jinkirta cire tallafin man fetur har zuwa karshen mulkinsa a 2023 domin ya hada ’yan Najeriya fada da Tinubu.

Kazalika, ’yan Najeriya sun rika sukar lamirin gwamnatin Tinubu kan kawo wahalhalu da yunwa tun bayan sanar da cire tallafin man da shugaban ya yi ranar da aka rantsar da shi.

To sai dai Garba Shehu ya karyata batun cewa an shirya cire tallafin ne saboda a yi wa Tinubu zagon kasa.

Kakakin ya ce ya cika da mamakin labarin, yana mai cewa ba yadda za a yi Buhari ya yi hakan ga dan jam’iyyarsa, tamkar daga wata jam’iyyar zai karbi mulkin daga hannunsa.

Ya ce, “Da Buhari da Tinubu duk ’yan APC ne, saboda haka ban ga ta yadda za mu shirya abin da zai yi wa gwamnatinmu zagon kasa ba.

“Buhari mutum ne da ya tsani harkar rashawa, ya shigo gwamnati da gaskiyar shi, kuma har ya gama a haka yake. Ya yi iya bakin kokarinsa ga ’yan Najeriya kuma tarihi ba zai manta da shi ba. shi ba mutum ba ne mai kwarmato, aiki kawai ya yi,” in ji Garba Shehu.

Ya kuma ce shi a karan kansa bai yi laifi ba saboda ya kyale tsohon maigidansa kuma tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya yi aiki a gwamnatin Buhari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari Garba Shehu Garba Shehu

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da cibiyar Fasaha ta Zamani ta Arewa maso Yamma da hukumar sadarwa ta ƙasa (NCC) ta gina a Kano, wadda matasa suka lalata a lokacin zanga-zangar ƙuncin rayuwa ta #EndBadGovernance a watan Agustan 2024. Ministan Harkokin Sadarwa Dr. Bosun Tijani, ne ya wakilci shugaban ƙasa a wajen bikin ƙaddamarwar.

A jawabin sa, Minista Tijani ya bayyana cewa wannan katafaren aiki da gwamnatin Tinubu ta samar ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, zai iya zama babbar hanya ga matasa su tsira daga talauci idan har suka yi amfani da damar yadda ya kamata. Ya bayyana damuwarsa kan lalata cibiyar mako guda kafin a ƙaddamar da ita, duk da cewa an kammala aikin tun watan Janairu.

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

Ministan ya ce lokacin da ya samu labarin lalata cibiyar, bai bar fushinsa ya hana shi sake ci gaba da aikinta ba. Ya tuntuɓi kamfanoni kai tsaye don a gyara cibiyar cikin gaggawa ba tare da dogon tsarin gwamnati ba. Ya kara da cewa shirin cibiyar na da burin samar da  ƙwararrun matasa miliyan uku da za su samu horo a fannin fasaha, domin samun damar ci gaba da kuma shiga kasuwannin duniya.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ta bakin mataimakinsa Abdussalam Gwarzo, ya ce jihar na da shirin horas da matasa 300,000 kan fasahar zamani nan da shekarar 2027. Ya bayyana cewa tuni aka fara horar da ma’aikatan gwamnati 5,000 da suka samu ƙwarewa a fannin fasaha. Shugaban hukumar NCC, Dr. Aminu Maida, ya ce wannan cibiya ta fasaha na daga cikin dabarun raya tattalin arziƙin dijital na ƙasa, kuma za ta taimaka matuƙa wajen haɓaka ƙwarewar matasan jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
  • Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina