Aminiya:
2025-07-01@01:57:46 GMT

Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi

Published: 1st, July 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Anambra, Peter Obi ya ce zai yi takarar shugabancin Nijeriya a 2027 domin ba zai shiga duk wata yarjejeniyar haɗakar takara da kowa ba.

Obi wanda ya yi takarar shugabancin Nijeriya a Zaben 2023 a karkashin inuwar jam’iyyar Labour (LP), ya tabbatar wa magoya bayansa cewa babu gudu babu ja da baya dangane da takararsa a babban zaɓen kasar na gaba.

An sanya dokar hana fita a Kaduna An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Sai dai ya ce idan har akwai wata yarjejeniya da zai kulla, ba za ta wuce wacce za ta ba shi damar zama shugaban ƙasa na wa’adi daya ba, sannan ya miƙa wa shugaba na gaba mulki a ranar 28 ga watan Mayun 2031.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya fitar, Obi ya bayyana hakan a yayin amsa tambayoyin magoya bayansa  wata hira ta kai tsaye da aka yi da shi a shafin X a ranar Lahadi.

Obi ya musanta kulla yarjejeniyar tsayawa takara a karkashin tikiti daya da tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar.

Haka kuma, Obi ya ce duk wata haɗaka da za a yi wadda ba ta da kudirin kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihohin Benuwe da Zamfara…da kuma bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, to kuwa babu shi babu ita.

Kazalika, Obi ya ce yana goyon bayan tsarin da zai bayar da damar a rika karɓa-karɓar mulki a tsakanin Kudu da Arewacin Nijeriya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara

Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce zai iya yin komai muddin hakan zai kawo zaman lafiya da ci gaba a jiharsa.

Fubara, ya faɗi haka ne a garin Fatakwal a ranar Asabar, yayin da yake magana da magoya bayansa.

An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City

Ya tabbatar musu cewa ya sasanta da Tsohon Gwamnan jihar, wanda a yanzu Ministan Abuja ne, Nyesom Wike.

Ya ce ya san wasu daga cikin magoya bayansa ba za su ji daɗin sasancin da aka yi ba, amma ya roƙe su da su yi haƙuri.

Ya ce: “Wani lokaci sai an ɗauki matakai masu wahala domin a samu gyara.”

Ya ƙara da cewa: “Kowa ya san mun yi iya ƙoƙarinmu. Amma yanzu abin da muke buƙata shi ne zaman lafiya.”

Fubara ya ce ba wanda zai iya musanta irin taimakon da Wike ya masa.

“E, mun samu saɓani a wasu abubuwa, amma ba za a iya cewa Wike bai taka rawar gani ba.

“Duk wanda ke sona da gaskiya, ya daina magana, lokaci ne na zaman lafiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje
  • Yau za a yi Jana’izar Aminu Dantata a Madina
  • Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
  • Kebbi: PDP za ta yi haɗaka don ƙalubalantar APC a zaɓen 2027
  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
  • Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
  • Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan