Aminiya:
2025-08-17@11:16:48 GMT

DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

Published: 2nd, July 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Burodi ya zama daya daga cikin abincin da ‘yan Najeriya basa iya yi babu shi. Yayin da wasu ke cin shi a matsayin abin Karin kumallo da safe, wasu kuwa na cin shi a matsayin abincin rana a wasu lokutan ma har da na dare.

 

A duk lokacin da aka ce masu sarrafa burodi sun shiga yajin aiki, ko fulawa tayi karanci hakan kan haifar da raguwar burodi a kasuwa wadda kan jefa masu cin shi a cikin mawuyacin hali.

NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Shirin Najeriya A Yau na wannan makon zai yi nazari ne kan sinadaran da ake amfani da su wajen sarrafa burodi da kuma irin cutar da suke jawowa.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: sinadaran burodi

এছাড়াও পড়ুন:

An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

Shugaban hukumar kula da wasanni ta ƙasa (NSC), Bukola Olopade, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa Super Falcons ba su samu kuɗin alawus ɗin da aka yi musu alƙawari ba, yana mai cewa an riga an biya duk ƴan wasan, sai kaɗan daga cikinsu da ke da matsalar asusun banki. Ya ce ya tabbatar da hakan ne daga shugabar ƙungiyar, Rasheedat Ajibade, da kuma hukumar kwallon ƙafa ta ƙasa (NFF).

Olopade ya ce ba daidai ne a yi iƙirarin cewa ba a biya kuɗin ba, inda ya ƙara da cewa bai kamata a jefa Ajibade cikin matsalar musanta kalaman da ba ta faɗa ba. Ya bayyana cewa waɗanda ke da matsalar asusun banki su kaɗai ba su samu ba, amma sauran duk sun karɓi hakkokinsu.

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Game da kyautar $100,000 da gidajen masu ɗakuna uku da Shugaba Bola Tinubu ya yi wa kowacce ƴar wasa bayan lashe kofin WAFCON na 2025, Olopade ya ce gwamnati na kan shirin cika alƙawarin nan da ba da komawa ba. Ya bayyana cewa ana ci gaba da tattaunawa da ma’aikatar gidaje da shirin Renewed Hope Homes domin ganin an kammala aikin cikin lokaci.

Ya jaddada cewa gwamnatin Tinubu tana da tarihin cika alƙawari ga ƴan wasa, inda ya ce ba sa sakaci da batun lada ko shirin tura su gasar ƙasa da ƙasa. A ranar 28 ga Yuli, 2025, Shugaba Tinubu ya karɓi tawagar Super Falcons a Fadar Aso Rock, inda ya sanar da kyautar kuɗi, da gida, da lambar yabo ga kowacce ƴar wasa, lamarin da daga baya ya jawo ce-ce-ku-ce bayan rahoton da aka danganta wa Ajibade.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Yadda zaɓen cike gurbi ke gudana a sassan Najeriya
  • Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
  • Wata Kotun kasar Canada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
  • Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya