Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau
Published: 28th, June 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Filato ba ta aiko da wani wakili zuwa Zariya domin yi wa iyalan waɗanda aka kashe a Ƙaramar Hukumar Mangu a Jihar Filato, ta’aziyya ba.
Aminiya ta ruwaito, yadda wasu matasa suka farmaki motar wasu ’yan ɗaurin aure su 31, inda suka kashe 13 daga cikinsu.
Sarkin ya bayyana hakan ne lokacin da jagoran shugabannin addinai, Tsohon Ministan Matasa da Wasanni Solomon Dalung, ya jagoranci wata tawaga zuwa fadarsa domin yin ta’aziyya.
Sarkin ya gode wa tawagar bisa wannan ziyara, amma ya nuna damuwa cewa babu ko ɗaya daga cikin wakilan Gwamnatin Filato da ya zo domin yin ta’aziyya ko duba halin da iyalan mamatan ke ciki.
Ya roƙi Gwamnatin Filato da ta ɗauki matakin gaggawa, kuma a tabbatar da adalci.
Haka kuma, ya jaddada buƙatar haɗin kai a tsakanin al’ummar Arewacin Najeriya bai ɗaya, tare da kiran shugabanni su haɗa kai domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Solomon Dalung, ya ce sun zo domin yi wa al’ummar da abin ya shafa da kuma masarautar Zazzau ta’aziyya.
Ya nemi a kwantar da hankali, sannan ya buƙaci gwamnati ta hukunta masu laifin.
Fasto Yohanna Buru, ɗaya daga cikin tawagar, ya bayyana harin a matsayin abin kunya.
Ya kuma ce ya zama dole a cafke masu hannu a harin.
Tawagar ta kuma kai ziyara ga Farfesa Ango Abdullahi kafin su gana da Sarkin Zazzau.
Fasto George T. John, wani daga cikin tawagar, ya ce al’ummar da abin ya shafa na cikin baƙin ciki sosai.
Ya yi Allah-wadai da harin, yana mai cewa hakan mummunan laifi ne.
Yakubu Yusuf, ɗaya daga cikin ’yan uwan waɗanda aka kashe daga Angwan Dantsoho a Ƙaramar Hukumar Kudan, ya gode wa baƙin.
Ya kuma roƙi gwamnatin jihar da ta Tarayya da su taimaka wa marayu da mamatan suka bari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kisan Yan Ɗaurin Aure
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya ce yaki da talauci muhimmin mataki ne na hanzarta ci gaban tattalin arziki da samar da ayyukan yi.
Ya bayyana haka ne a lokacin shirin gwamnatin jihar mai taken “Gwamnati da Jama’a” wanda aka gudanar a karamar hukumar Ringim.
Malam Umar Namadi ya jaddada muhimmancin horas da matasa sana’o’in hannu da samar da yanayin kasuwanci mai kyau domin cimma wadannan manufofi.
Saboda haka, ya yi kira ga zababbun wakilai, masu rike da mukaman siyasa, shugabannin kasuwanci da sauran attajirai da su taimaka wa al’ummarsu domin kara bunkasa ci gaba da habaka tattalin arziki.
A yayin taron, Kwamishinan jin kai da harkokin musamman na jihar, Auwal Danladi Sankara, ya raba naira miliyan 50 a matsayin tallafin karfafa gwiwa ga matasa da mata sama da 250.
A cewarsa, wannan shirin tallafin kudi na musamman an kirkiro shi ne domin tallafawa kokarin Gwamna Umar Namadi wajen samar da ayyukan yi ga matasa, kirkiro sabbin ayyuka da kuma rage talauci a jihar.
Ya kara da cewa, an tsara tallafin kudin ne domin wasu su fadada kasuwancinsu, yayin da wasu kuma za su fara sabon kasuwanci na zabinsu.
Ya ce kowanne daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin ya samu naira dubu dari biyu da hamsin (₦250,000), tare da yin alkawarin ci gaba da mara wa shirin manufofi 12 na Gwamna Namadi baya, wanda aka tsara domin tabbatar da arziki da ci gaba a Jihar Jigawa.
Usman Mohammed Zaria