Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau
Published: 28th, June 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Filato ba ta aiko da wani wakili zuwa Zariya domin yi wa iyalan waɗanda aka kashe a Ƙaramar Hukumar Mangu a Jihar Filato, ta’aziyya ba.
Aminiya ta ruwaito, yadda wasu matasa suka farmaki motar wasu ’yan ɗaurin aure su 31, inda suka kashe 13 daga cikinsu.
Sarkin ya bayyana hakan ne lokacin da jagoran shugabannin addinai, Tsohon Ministan Matasa da Wasanni Solomon Dalung, ya jagoranci wata tawaga zuwa fadarsa domin yin ta’aziyya.
Sarkin ya gode wa tawagar bisa wannan ziyara, amma ya nuna damuwa cewa babu ko ɗaya daga cikin wakilan Gwamnatin Filato da ya zo domin yin ta’aziyya ko duba halin da iyalan mamatan ke ciki.
Ya roƙi Gwamnatin Filato da ta ɗauki matakin gaggawa, kuma a tabbatar da adalci.
Haka kuma, ya jaddada buƙatar haɗin kai a tsakanin al’ummar Arewacin Najeriya bai ɗaya, tare da kiran shugabanni su haɗa kai domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Solomon Dalung, ya ce sun zo domin yi wa al’ummar da abin ya shafa da kuma masarautar Zazzau ta’aziyya.
Ya nemi a kwantar da hankali, sannan ya buƙaci gwamnati ta hukunta masu laifin.
Fasto Yohanna Buru, ɗaya daga cikin tawagar, ya bayyana harin a matsayin abin kunya.
Ya kuma ce ya zama dole a cafke masu hannu a harin.
Tawagar ta kuma kai ziyara ga Farfesa Ango Abdullahi kafin su gana da Sarkin Zazzau.
Fasto George T. John, wani daga cikin tawagar, ya ce al’ummar da abin ya shafa na cikin baƙin ciki sosai.
Ya yi Allah-wadai da harin, yana mai cewa hakan mummunan laifi ne.
Yakubu Yusuf, ɗaya daga cikin ’yan uwan waɗanda aka kashe daga Angwan Dantsoho a Ƙaramar Hukumar Kudan, ya gode wa baƙin.
Ya kuma roƙi gwamnatin jihar da ta Tarayya da su taimaka wa marayu da mamatan suka bari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kisan Yan Ɗaurin Aure
এছাড়াও পড়ুন:
Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.
Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.
Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaroRahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.
Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.
Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.
Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.
Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.