2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Published: 29th, June 2025 GMT
Wannan ne ma dalilin da yasa wasu ke ganin hadakar za ta iya yin karfi kwarai da gaske, kasancewar ta samu wakilci a sassa daban-daban na wannan kasa.
Dalili kuwa shi ne, ‘yansiyasa ne da a baya suka samu damar rike manya-mnyan mukamai, sannan kuma har zuwa yanzu yana da tasiri a fagen siyasar kasar yadda ya kamata.
Manya-manyan jiga-jigan da ake gani a cikin wannan sabuwar tafiya ta hadakar jam’iyyar sun hada da:
Jagoran adawa a kasar, wanda a baya ya sha yin takarar shugabancin kasa, sannan kuma ko a shekarar 2023 shi ne ya zo na biyu bayan da ya samu kuri’a kusan miliyan bakwai.
Alhaji Atiku Abubakar, wanda a yanzu dan jam’iyyar PDP ne; ya kasance guda kuma jigo a siyasar Nijeriya, tun lokacin da ya zama mataimakin shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo a shekarar 1999 zuwa 2007.
Tsohon mataimakin shugaban kasar, wanda ya fito daga Jihar Adamawa da ke Arewa maso gabashin Nijeriya, Bafulatani ne da ake yi wa kallon daya daga cikin masu matukar tasiri a fagen siyasar Nijeriya.
Atiku, na daga cikin fitattun mutanen da suka kulla wannan hadaka da ta haifar da jam’iyyar APC a shekarar 2014, da ta yi nasarar kwace mulki daga hannun jam’iyyar PDP a 2015.
A halin da ake ciki yanzu dai, jam’iyyar PDP na da gwamnoni kimanin 10 a fadin wannan kasa, koda-yake dai kuma, har yanzu babu gwamnan da ya bayyana amincewa da bin Atikun zuwa sabuwar jam’iyyar hadakar, duk da dai ana ganin watakila ficewar tasa za ta sa wasu daga cikin gwamnonin ficewa su su bi shi.
Haka zalika, tsohon dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar LP, na daya daga cikin mutane na gaba-gaba a kafa wannan sabuwar tafiyar ta jam’iyyar ADA.
Peter Obi , wanda tsohon Gwamnan Jihar Anambra ne, ya kasance na uku a zaben shugaban kasar da ta gabata a 2023, inda ya samu kuri’a fiye da miliyan shida.
Obi, dan asalin kabilar Igbo ne daga Kudu maso gabashin wannan kasa, wanda da ya samu farin jini yadda ya kamata, musamman a tsakanin ‘yan kabilarsa.
Wannan dalili ne ma yasa ake ganin jam’iyyar tasa ta LP ta samu nasara a jihohin kasar nan 12, ciki har da Jihar Legas da Abuja a zaben shugaban kasar na 2023.
Kazalika, jam’iyyarsa ta LP na da gwamnan guda daya a Jihar Abia, sannan kuma ana ganin watakila ya bi shi cikin wannan sabuwar hadaka da ake shirin yi.
Har wa yau, a watan Maris da ya gabata ne Malam Nasiru el-Rufai ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC tare da kuma da komawa jam’iyyar SDP.
Tsohon gwamnan, ya kasance Ministan Abuja a tsakanin shekara ta 2003 zuwa 2007, kafin ya zama gwamnan Jihar Kaduna da ke Arewa maso yammacin kasar, na tsawon wa’adi biyu, wato tsakanin 2015 zuwa 2023.
Fitaccen ɗan siyasar, a kakar zaben 2023; wanda Bahaushe ne dan asalin garin Zaria, ya kasance na gaba-gaba wajen goyon bayan Bola Ahmed Tinubu na APC.
Sai dai kuma, bayan lashe zaben na Tinubu; sai kuma baraka ta kunno kai a tsakaninsa da Nasiru, bayan da majalisar dattawa ta ki amincewa da tantance shi, domin ba shi mukamin minista a gwamnatin ta Tinubu.
Rotimi Amaechi, shi ma guda ne cikin tsofaffin hannu a bangaren siyasar wannan kasa, domin kuwa ya kasance tsohon Gwamnan Jihar Ribas mai arzikin mai fetur da ke yankin Kudu maso kudancin wannan kasa daga 2007 zuwa 2015.
Haka nan, bayan kammala wa’adinsa a matsayin Gwamnan Jihar Ribas din, tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya nada shi ministan sufuri na tsawon shekara takwas daga 2015 zuwa 2023.
Har ila yau, A shekarar 2022 ya bayyana anisarya ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023, to amma kuma sai ya sha kaye a hannun Tinubu a zaben fitar da gwani.
A wata hira da ya yi da BBC a baya-bayan nan, tsohon ministan ya ce; a shirye yake domin shiga duk wata hadakar da za ta kawar da gwamnatin Tinubu a halin yanzu.
A gefe guda kuma, Rauf Aregbesola ya taba rike mukamin Gwamnan Jihar Osun da ke Kudu maso yammacin Nijeriya, har na tsawon wa’adi biyu daga 2010 zuwa 2018.
A shekarar 2019, tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya nada shi, mukamin ministan harkokin cikin gida, mukamin da ya rike har 2023.
Aregbesola Bayerabe ne da ya fito daga yankin Kudu maso yammacin Nijeriya.
A farkon shekarar nan ne, Rauf Aregbesola ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar ta APC.
Tsohon jami’in soji, wanda ya taba zama Gwamnan Mulkin Soji na Jihar Neja daga 1984 zuwa 1986, Dabid Mark; dan asalin Jihar Benuwai ne.
Kazalika, ya rike mukamin ministan sadarwa; kafin ya zama dan majalisar dattawa mai wakiltar Benuwai ta Kudu a cikin jihar ta Benuwai.
Har ila yau, shi ne Shugaban Majalisar Dattawa mafi jimawa a mukamin, bayan jagorantar majalisar na tsawon wa’adi biyu, wato shekara takwas daga 2007 zuwa 2015.
Sannan, ya kasance dan asalin kabilar Idoma daga yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya, shi ma yana cikin wannan hadakar jam’iyyar adawa, dumu-dumu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: shugaban kasar gwamnan Jihar Gwamnan Jihar wannan kasa
এছাড়াও পড়ুন:
Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar.
Murabus ɗin nasa ya fara aiki nan take.
Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a GombeGanduje, wanda tsohon Gwamnan Jihar Kano ne, ya bayyana rashin lafiya a matsayin dalilin da ya da ya ajiye muƙaminsa.
Ganduje ya zama Shugaban APC a watan Agustan 2023, a lokacin da jam’iyyar ke fama da rikicin cikin gida.
Lokacin da ya kwashe a matsayin shugaban jam’iyyar na cike da cece-kuce da suka.
Dalilin murabus ɗinsaKo da yake Ganduje ya ce rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus, wasu majiyoyi sun bayyana cewa rikicin siyasa a cikin jam’iyyar ne suka tilasta masa ajiye muƙamisa.
Haka kuma, an danganta murabus ɗinsa da zarge-zargen almundahana da karkatar da kuɗaɗe.
Wasu ’ya’yan jam’iyyar sun koka cewa ofishinsa na tilasta musu biyan kuɗi da yawa, musamman masu neman tikitin takara a Abuja.
Tasirin murabus ɗinsa ga jam’iyyar APCMurabus ɗin Ganduje babban sauyi ne ga shugabancin jam’iyyar APC.
Yanzu haka, mutane da dama suna jiran su ji yadda jam’iyyar za ta shawo kan wannan lamari.
Har yanzu jam’iyyar APC ba ta fitar da wata sanarwa kan murabus ɗinsa ba.
Matsalolin da suka shafi Ganduje kan shugabancin jam’iyyarA farkon shekarar 2024, wata kotu a Jihar Kano ta hana Ganduje ci gaba da kiran kansa da ɗan jam’iyyar APC, bayan wasu shugabannin jam’iyyar sun shigar da ƙara a kansa.
Daga baya kuma, wata kotu a Abuja ta yi watsi da ƙarar da wasu ke yi don a tsige shi daga shugabancin jam’iyyar.
Zamanin Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar cike yake da rikice-rikice, kuma murabus ɗinsa yanzu zai sanya dasa ayar tambayoyi domin neman wasu amsoshi.