Aminiya:
2025-10-13@19:36:22 GMT

Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai

Published: 3rd, July 2025 GMT

Amurka ta dakatar da tallafin makaman da take bai wa Ukraine, tana mai bayyana damuwa kan raguwar makamanta a rumbun adana su.

Mai magana da yawun Fadar Gwamnatin Amurka, Anna Kelly a watan sanarwar da ta fitar, ta ce a halin yanzu muradun Amurka ne kan gaba ta bangaren tsaro, don haka dole ne ta dakatar da duk wani tallafin makamai da take bai wa Ukraine din.

Hamas ta karɓi tayin tsagaita wuta a Gaza Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Rasha ke ci gaba da fadada hare-harenta a kan kasar, yayin da aka kwashe sama da shekaru biyu ana gwabza yaki tsakanin kasashen da ke makwabtaka da juna.

Rahotanni na cewa, Ukraine za ta shiga tsaka mai wuya, musamman yadda za ta ci gaba da fuskantar Rasha ba tare da irin makaman Amurka ba,  yayin da Shugaba Vladimir Putin, ya shawarci Ukraine din da ta mika wuya.

Tuni aka shiga damuwa a wannan kasa da ke gabashin Turai, inda gwamnatin kasar ke ganin daga lokacin da aka fara samun tsaikon tallafin Amurka, Rasha za ta kara samun kwarin gwiwar kai farmaki babu kakkautawa.

A halin da ake ciki Ukraine ta shiga tsaka mai wuya, domin baya ga katse tallafin makamai, matakin da shugaba Trump ya dauka na dakatar da ayyukan Hukumar Raya Ƙasashe ta Amurka, ya shafi ayyukan jin kai a wannan kasa, sakamakon cewa tana cikin kasashen da suke karbar tallafin USAID sosai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rasha Ukraine

এছাড়াও পড়ুন:

Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa

 

‘Yan sa’o’i kafin sanarwar da Jam’iyyar ta RN ta yi ne dai, tsohon Firaministansa Edouard Philippe ya ce yana goyon bayan shirya sabon zaben shugaban kasa a gaggauce.

 

Wannan matsin lamba dai kari ne kan wadda shugaban na Faransa ke fusakanta daga bangaren masu sassaucin ra’ayi, wadanda su kuma bukatarsu ita ce a zabi sabon Firaminista daga cikinsu.

 

Sai dai a iya cewa akwai ragowar fatan kawo karshen rudanin da siyasar Faransar ta shiga, la’akari da bayanan da suka ce a dazu an shiga tattaunawa tsakanin jagoran jam’iyyar masu ra’ayin ‘yan mazan jiya Bruno Retailleau da Firaminista Lecournu, kwana guda bayan murabus din da ya yi. Yayin da kuma a gefe guda rahotanni suka ce a gobe Laraba wakilan masu sassaucin ra’ayi na jam’iyyar Socialist za su gana da Firaminista Lecournun mai murabus.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya? October 12, 2025 Manyan Labarai Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna  October 12, 2025 Rahotonni Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
  • Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato