Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Published: 1st, July 2025 GMT
Hukumar kiwon lafiya ta kasar Sin, ta yi watsi da bangaren rahoton kwamitin SAGO, na masana kimiyya mai bayar da shawara game da asalin kwayar cutar da ta haddasa annobar COVID-19, wanda hukumar lafiya ta duniya WHO ta fitar.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar a Litinin din nan, ta ce a ranar 27 ga watan Yunin nan, kwamitin SAGO, ya wallafa wani rahoto game da tushen kwayar cutar SARS-CoV-2, wadda ta haddasa barkewar annobar COVID-19.
Sanarwar ta ce, duk da yake bincike mai zaman kansa da kwamitin SAGO ya gudanar bai nuna wata sabuwar shaida game da asalin kwayar cutar ba, bai kuma bayyana wani abu da ya saba da sakamakon binciken hadin gwiwa tsakanin Sin da WHO na watan Maris din shekarar 2021 ba, a hannu guda, wasu kasashe da daidaikun mutane sun shigar da harkalla, da tasirinsu cikin rahoton, wanda daga karshe ya kunshi bayanai marasa tushe daga jita-jita, wadanda suka yi matukar suka ga nagartattun bayanan kimiyya dake cikin rahoton mai tushe da aka riga aka gabatar.
Kazalika, rahoton na SAGO ya kunshi wasu bukatu marasa tushe kan kasar Sin, kamar dai yadda sanarwar ta hukumar kiwon lafiya ta kasar Sin ta bayyana. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
Al’ummar Ƙaramar Hukumar Isa da ke Jihar Sakkwato, sun roƙi gwamnatin jihar da ta Tarayya da jami’an tsaro da su kai musu ɗauki kan barazanar da ƙasurgumin ɗan bindiga Bello Turji ke musu.
A farkon makon nan ne aka samu labarin cewa Bello Turji ya bai wa mazauna wasu yankuna a Isa wa’adin gina masa ƙaramin dam ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.
Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a MadinaHar ila yau, ya umarce su da su bar garuruwansu, domin ba ya buƙatar ganinsu a wajen.
Wani mazaunin yankin, Wanzami Abubakar Isa, ya bayyana damuwarsa cewa suna zaune garuruwansu kamar baƙi.
“Abin takaici ne yadda ’yan bindiga ke ba mu umarni a garinmu na haihuwa. Muna roƙon gwamnati ta taimake mu.“
Shi ma Alhaji Abdullahi Isa ya ce, “Rayuwarmu ta shiga mawuyacin hali. Ba za mu iya ci gaba da rayuwa a haka ba.
“Ta yaya za mu bar gidajenmu saboda barazanar ɗan bindiga? Gwamnati ta yi wani abu cikin gaggawa.”
Wani mazaunin yankin, Bashar Ahmad, ya ce ba daidai ba ne a bar Turji yake cin karensa babu babbaka.
“Gwamnati ta kare mu, mu ma ’yan ƙasa ne kuma muna da ’yancin zama lafiya.”
Sai dai duk ƙoƙarin jin ta bakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Isa, Alhaji Sharifu Kamarawa, da mai bai wa gwamna shawara kan harkar tsaro, Ahmad Usman, bai yi nasara ba, domin ba su amsa kira ko saƙon da aka aike musu ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Yanzu haka, ko da yake Turji bai bayyana ranar da zai kai hari ba, akwai fargaba sosai a yankin.
Jama’a na ganin ya kamata gwamnati ta ɗauki mataki mai tsauri, maimakon ci gaba da yin sulhu da ’yan bindigar da ke addabar yankin gabashin Sakkwato.