SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)
Published: 18th, May 2025 GMT
A wancan lokacin, Sarkin Abuja shi ne Marigayi Sulemanu Barau, wanda ya rasu a shekarar 1979. Saboda hikimarsa da hangen nesa, ya ga cewa zai fi dacewa mutanensa su samu ‘yanci da asali ta hanyar kasancewa cikin wata jiha a kasar tarayya, fiye da su kasance a cikin wani yanki da ake kira kasar kowa ba tasa ba, kamar yadda ake kallon FCT a yanzu.
A sakamakon haka, kashi 80 cikin dari na kasar da ke karkashin Masarautar Abuja da sunanta gaba-daya, aka mika wa gwamnatin tarayya domin gina FCT. Wannan kaso ya yi daidai da 80 cikin dari na jimillar fadin FCT a yanzu. Sauran kashi 20 cikin dari kuwa, an samo su ne daga tsohuwar Jihar Filato da tsohuwar Jihar Kwara, wato Nasarawa da Kogi a halin yanzu.
Daga baya kuma, an sauya sunan garin zuwa Suleja a shekarar 1979, a girmama Marigayi Sulemanu Barau. sauran kasar 20 cikin dari yanzu su ne suka zama Kananan Hukumomin Suleja, Gurara da Tafa a Jihar Neja.
A karshe dai, yau dukkanin asalin mutanen Masarautar Suleja kafin kirkiro FCT, wato wadanda ke wajen FCT; amma cikin Jihar Neja da kuma ‘yan’uwansu daga kabilun Gbagyi, Koro da wasu da ke cikin FCT, sun zama tamkar marasa tushe ko makoma, suna kallon zuwan FCT a matsayin masifa maimakon albarka. Asalin mazauna FCT, na fafatawa da sauran ‘yan Nijeriya wajen mallakar kasa, wadanda ke da karfi na kudi da tasiri fiye da su.
‘Yan Nijeriya na da fa’ida biyu, zai iya zama dan asalin jiharsa kuma ya nemi mukami ko kujerar siyasa a nan da kuma FCT. Amma dan asalin FCT, ba zai iya samun irin wannan dama a wasu jihohi ba, saboda za a dauke shi a matsayin bako.
Haka kuma, dukkanin mutanen Jihar Neja da ma sauran ‘yan Nijeriya na gasa da mutanen Suleja wajen mallakar kasa a Suleja, saboda kusancinta da babban birnin tarayya, muddin suna da karfin kudi da goyon bayan gwamnati daga Minna. Duk da haka, ta halin da ake ciki da dabi’ar mutane, kowa ya fi jin dadin zama a kasarsa fiye da kasar da ba tasa ba.
Asalin mazauna Abuja ko da suna cikin Suleja ko FCT, sun takaita ne kawai a yankunansu, suna cikin gasa mai tsauri da sauran ‘yan Nijeriya. Hanyarsu mafi rinjaye ta samun abinci, ita ce noma, amma mallakar gonaki da gidaje a kauyukansu yanzu ya zama tarihi. Yawancin matasa ba su da karfin saye, sai dai su kama haya a garuruwansu, domin zama da iyalinsu; abin da yawancin al’umma ke kallo tamkar sabo da al’ada. Abin da ake tsoro da yake faruwa a FCT yanzu, ya fara bayyana har ma a makwabciyarta, Suleja.
Halin da suka ci gaba da shiga ya karu ne sakamakon jahilci da kin neman ilimi daga wasu, wadanda ke yada karya ga jama’a. Wani tsohon dan jarida ya rubuta a jaridar Sunday Tribune ta 28 ga Janairu 2024 cewa, gwamnatin tarayya ta biya diyyar asalin mazauna FCT, kuma ta gina musu Suleja. Wannan na nufin cewa; har ma tsofaffin ‘yan jarida da dattawan kasa suna da fahimta maras tushe cewa, Suleja ginin gwamnatin tarayya ne bayan kirkiro FCT.
Tambayoyin da suka dace a yi su ne; ko an biya Suleja diyya ne dangane da kafa FCT? Ko kuwa ana ba mazaunanta kulawa daidai da sauran al’ummomin Jihar Neja, wajen samar da ababen more rayuwa da ayyuka? Idan FCT na da fa’idodi, wa ke amfana da su, Suleja ko jihar?
Za mu ci gaba a mako mai zuwa
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yan Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Batun kare hakkin bil’adama da ake yi a duniya ba komai ba ne sai karya.
Shugaba Fizishkiyan ya yi ishara da yadda masu ikirarin kare hakkin bil’adama suke sa kafafunsu suna take hakkin mutanen Gaza da cikin kasashen yammacin Asiya da kuma tafka manyan laifuka.
A yau Talata ne dai shugaban kasar ta Iran ya gabatar da jawabi a wurin bikin girmama shahidan kallafaffen yaki na kwanaki 12, ya bayyana cewa: “A cikin wannan duniyar wacce take riya ci gaba da wayewa, a gaba idon duniya, ake yanke wa mutanen Gaza ruwan sha da abinci, a hana mata da kananan yara. Haka nan kuma ake tafka laifukan da su ka kunshi kisan kiyashi, amma kuma wai su ne ke Magana akan kare hakkin bil’adama.”
Shugaban kasar ta Iran ya kuma ce, masu yin Magana akan kare hakkin bil’adama din ne suke sa kafafunsu suna take shi.
Shugaban kasar ta Iran ya kuma ce, HKI da Amurka, sun kawo hari bisa riya cewa Iran tana son kera makamin Nukiliya, kuma wadanda su ka kai wa harin mata ne, kananan yara da kuma sauraren hula da ba su da makamai.
Shugaban kasar ta Iran ya ambato hudubar da Imam Hussain ( a.s) ya yi wa abokan gabarsa a karbala cewa: “Idan ba ku da addini, to ku zama ‘yantattun a cikin harkokinku na duniyu.”
Shugaba Fizishkiyan ya kara da cewa: A wannan lokacin suna yanke abinici da ruwa ga mutanen Gaza, sannan kuma a lokaci daya suna Magana akan kare hakkin bil’adama. Wane annabi ko addinin Allah ne ya halarta tafka laifuka irin wannan ?