SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)
Published: 18th, May 2025 GMT
A wancan lokacin, Sarkin Abuja shi ne Marigayi Sulemanu Barau, wanda ya rasu a shekarar 1979. Saboda hikimarsa da hangen nesa, ya ga cewa zai fi dacewa mutanensa su samu ‘yanci da asali ta hanyar kasancewa cikin wata jiha a kasar tarayya, fiye da su kasance a cikin wani yanki da ake kira kasar kowa ba tasa ba, kamar yadda ake kallon FCT a yanzu.
A sakamakon haka, kashi 80 cikin dari na kasar da ke karkashin Masarautar Abuja da sunanta gaba-daya, aka mika wa gwamnatin tarayya domin gina FCT. Wannan kaso ya yi daidai da 80 cikin dari na jimillar fadin FCT a yanzu. Sauran kashi 20 cikin dari kuwa, an samo su ne daga tsohuwar Jihar Filato da tsohuwar Jihar Kwara, wato Nasarawa da Kogi a halin yanzu.
Daga baya kuma, an sauya sunan garin zuwa Suleja a shekarar 1979, a girmama Marigayi Sulemanu Barau. sauran kasar 20 cikin dari yanzu su ne suka zama Kananan Hukumomin Suleja, Gurara da Tafa a Jihar Neja.
A karshe dai, yau dukkanin asalin mutanen Masarautar Suleja kafin kirkiro FCT, wato wadanda ke wajen FCT; amma cikin Jihar Neja da kuma ‘yan’uwansu daga kabilun Gbagyi, Koro da wasu da ke cikin FCT, sun zama tamkar marasa tushe ko makoma, suna kallon zuwan FCT a matsayin masifa maimakon albarka. Asalin mazauna FCT, na fafatawa da sauran ‘yan Nijeriya wajen mallakar kasa, wadanda ke da karfi na kudi da tasiri fiye da su.
‘Yan Nijeriya na da fa’ida biyu, zai iya zama dan asalin jiharsa kuma ya nemi mukami ko kujerar siyasa a nan da kuma FCT. Amma dan asalin FCT, ba zai iya samun irin wannan dama a wasu jihohi ba, saboda za a dauke shi a matsayin bako.
Haka kuma, dukkanin mutanen Jihar Neja da ma sauran ‘yan Nijeriya na gasa da mutanen Suleja wajen mallakar kasa a Suleja, saboda kusancinta da babban birnin tarayya, muddin suna da karfin kudi da goyon bayan gwamnati daga Minna. Duk da haka, ta halin da ake ciki da dabi’ar mutane, kowa ya fi jin dadin zama a kasarsa fiye da kasar da ba tasa ba.
Asalin mazauna Abuja ko da suna cikin Suleja ko FCT, sun takaita ne kawai a yankunansu, suna cikin gasa mai tsauri da sauran ‘yan Nijeriya. Hanyarsu mafi rinjaye ta samun abinci, ita ce noma, amma mallakar gonaki da gidaje a kauyukansu yanzu ya zama tarihi. Yawancin matasa ba su da karfin saye, sai dai su kama haya a garuruwansu, domin zama da iyalinsu; abin da yawancin al’umma ke kallo tamkar sabo da al’ada. Abin da ake tsoro da yake faruwa a FCT yanzu, ya fara bayyana har ma a makwabciyarta, Suleja.
Halin da suka ci gaba da shiga ya karu ne sakamakon jahilci da kin neman ilimi daga wasu, wadanda ke yada karya ga jama’a. Wani tsohon dan jarida ya rubuta a jaridar Sunday Tribune ta 28 ga Janairu 2024 cewa, gwamnatin tarayya ta biya diyyar asalin mazauna FCT, kuma ta gina musu Suleja. Wannan na nufin cewa; har ma tsofaffin ‘yan jarida da dattawan kasa suna da fahimta maras tushe cewa, Suleja ginin gwamnatin tarayya ne bayan kirkiro FCT.
Tambayoyin da suka dace a yi su ne; ko an biya Suleja diyya ne dangane da kafa FCT? Ko kuwa ana ba mazaunanta kulawa daidai da sauran al’ummomin Jihar Neja, wajen samar da ababen more rayuwa da ayyuka? Idan FCT na da fa’idodi, wa ke amfana da su, Suleja ko jihar?
Za mu ci gaba a mako mai zuwa
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yan Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.
A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.
Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFAYana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.
“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”
“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.
“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”
“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.