Hukumar samar da bunkasa da hadin gwiwar kasa da kasa ta kasar Sin ta gabatar da taron manema labarai a yau Juma’a, inda aka yi karin haske game da yadda Sin take baiwa kasashen Afirka tallafi da samun bunkasa tare da su cikin hadin gwiwa.

An ce, ya zuwa yanzu, Sin tana taimakawa kasashen Afirka fiye da 21 a bangaren kimiyyar aikin gona, inda ta tura musu kwararrun aikin gona fiye da 200.

Kazalika, bangarorin biyu suna hadin gwiwa wajen gudanar da ayyukan dake da nasaba da na’urorin wutar lantarki da horar da kwararru da habaka da karfinsu da sauran bangarori. Kana suna kaddamar da ayyukan samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, ciki har da samar da wutar lantarki ta amfani da karfin ruwa, da na hasken rana da samar da ruwa da sauransu.

Ban da wannan kuma, Sin ta taimaka wa kasashen Afirka wajen kara karfinsu na samun bunkasa. Kana ta riga ta horar da kwararrun ’yan Afirka fiye da dubu 15 tun bayan kiran taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da aka gudanar a bara a birnin Beijing. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Cibiyar binciken duniyar wata, karkashin hukumar kula da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya ta kasar Sin, ta sanar da cewa, zuwa karo na 9, kasar Sin ta samar da kasar duniyar wata da jimilar nauyinta ya kai gram 125.42, ga kwararru masu nazarin kimiyya da fasaha na kasashe daban daban, ciki har da kason kasar duniyar wata da aka raba ma wasu hukumomin bincike 7 na kasashe 6. Kana bisa gudanar da bincike kan kasar da na’urorin binciken duniyar wata na kasar Sin, wato Chang’e-5, da Chang’e-6, suka dawo da ita, masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin da na sauran kasashe, sun gabatar da sakamakon bincike fiye da 150.

An ce, tsarin da ake bi wajen neman samun kasar duniyar wata, shi ne a mika bukatar samun kasar ta wani shafin yanar gizo mai alaka da ayyukan binciken duniyar wata da sararin samaniya na kasar Sin. Daga baya wasu kwararru na kasar Sin za su tantance bukatar da aka mika, gami da yanke shawara kan ko za a ba da kasar ko a’a.

Ban da haka, bayanan da hukumar kula da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya ta kasar Sin ta samar, sun nuna yadda masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin ke karkata hankalinsu daga binciken labarin kasa na duniyar wata, zuwa na fasahar amfani da albarkatun duniyar wata, da samar da tubali don share fagen aikin gini a duniyar. A cewar wani jami’in hukumar kula da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya ta Sin, an yi hakan ne don shirya fasahohin da ake bukata wajen gudanar da ayyukan kai mutane duniyar wata, da gina tashar bincike kan duniyar wata, a nan gaba. (Bello Wang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Mali An Kama Sojoji Fiye da 40 Saboda Zargi da Kokarin Juyin Mulki
  • Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu
  • Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
  • Gwamna Bago Ya Kaddamar da Katafaren Kamfanin sarrafa Man Kade A Afirka.
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
  • Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan
  • Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza