Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Published: 28th, June 2025 GMT
Hukumar samar da bunkasa da hadin gwiwar kasa da kasa ta kasar Sin ta gabatar da taron manema labarai a yau Juma’a, inda aka yi karin haske game da yadda Sin take baiwa kasashen Afirka tallafi da samun bunkasa tare da su cikin hadin gwiwa.
An ce, ya zuwa yanzu, Sin tana taimakawa kasashen Afirka fiye da 21 a bangaren kimiyyar aikin gona, inda ta tura musu kwararrun aikin gona fiye da 200.
Ban da wannan kuma, Sin ta taimaka wa kasashen Afirka wajen kara karfinsu na samun bunkasa. Kana ta riga ta horar da kwararrun ’yan Afirka fiye da dubu 15 tun bayan kiran taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da aka gudanar a bara a birnin Beijing. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
Babbar Mai Shari’ar ta kasa , Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta jaddada cewa alkalai suna da nauyin tabbatar da adalci cikin gaskiya da daidaito a lokacin da matsalolin tattalin arziki ke kara tsananta wa al’umma.
Ta bayyana haka ne a Taron Alkalai na Shekara-shekara Karo na 26, wanda Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta shirya tare da haɗin gwiwar Cibiyar Koyar da Ayyukan Shari’a ta Kasa (NJI), a harabar Jami’ar da ke Kongo, Zariya.
Mai Shari’a Kekere-Ekun, wadda Sakatare na NJI, Barista Abdulazeez Aluwo ya wakilta, ta ce dole ne kotuna su yi hukunci da ke la’akari da yanayin tattalin arziki da kuma hakkokin masu nema da wadanda ake binsu hukunci.
Ta ce hakan ne kadai zai tabbatar da zaman lafiya da daidaiton al’umma.
Barista Abdulazeez Aluwo
CJN ta yi nuni da cewa rikice-rikicen harkokin kuɗi na zamani kamar hauhawar farashi da faduwar darajar naira, da canjin musayar kuɗi suna buƙatar tsantsar fassarar hukunce-hukuncen Shari’a bisa ilimi na zamani.
Ta yi kira da a kafa Kwamitin Tuntuba da zai kunshi Alkalai na kotu daukaka kara da Khadi da Manyan malamai na Shari’a da Kwararru a fannin kuɗi na zamani.
A cewarta, wannan kwamiti zai taimaka wajen ba kotuna jagoranci kan sabbin al’amuran da ke tasowa, tare da wayar da kan jama’a a kan dokokin kuɗin Shari’a.
Tun da farko, Daraktan Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci, Dakta. Sa’ad Abubakar, ya ce faduwar darajar kuɗi da hauhawar farashi suna barazana ga mu’amalar kasuwanci da aiwatar da shari’a.
Ya ce wannan al’amari na kara jefa kotunan Shari’a cikin matsaloli, musamman wajen tabbatar da adalci kan batutuwa masu alaƙa da mu’amaloli.
A sakonsa Mai martaba, Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli wanda Wazirin Zazzau Khadi Muhammad Inuwa Aminu ya wakilta, ya bukaci a hanzarta gyare-gyare a fannin Shari’a, musamman saboda yadda matsalar tattalin arziki ke shafar shari’o’in hul’i, da sadaki da dai sauransu.
Ana Shi bangare, Shugaban NJI, Mai Shari’a Babatunde Adejumo wanda Barista Zainab Salim ta wakilta ya yabawa sabon MOU da aka kulla tsakaninsu da ABU a fannin horaswa da bincike, da jagoranci da kuma inganta cancanta.
Ya ce taken taron na bana ya dace matuka, domin ya shafi manyan hakkoki na Shari’a kamar bashi da gado da sadaki, da mu’amaloli na yau da kullum.
Da yake Jawabi, Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Adamu Ahmad, Wanda Mataimakinsa a fannin Sha’anin Mulki Farfesa Suleiman Sabo ya wakilta ya ce taron alkalai na shekara–shekara muhimmin mataki ne da ke zurfafa tattaunawar shari’a da bunkasa bincike a fannin Shari’a a Najeriya.
A jawabinsa, tsohon Daraktan Cibiyar, Farfesa Muhammad Bello Usman, ya jaddada cewa adalci ba zai samu ba sai an dora nauyi da alhaki a kan mutanen da suka cancanta da kwarewa.
Taken Taron Shi ne : Shari’a a Yanayin Tattalin Arzikin Zamani: Tasirin Darajar Kuɗi da Canjin Musayar Kuɗi a Kan dokokin Shari’a.
Daga Ibrahim Suleiman