Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Ba Za A Iya Kawar Da Fasahar Nukiliya Da Karfi Ba
Published: 1st, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ba za a iya kawar da fasahar nukiliya ta hanyar harin bam ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arakchi ya jaddada cewa: Ba za a iya kawar da fasaha da kimiyyar da ake bukata don inganta sinadarin Uranium ta hanyar kai hare-haren bama-bamai ba.
A wata hira da ya yi da tashar talabijin ta CBS, Araqchi ya yi tsokaci kan ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na cewa ana iya komawa tattaunawa da Iran a cikin wannan mako: Araqchi yana mai mayar da martini da cewa: “Ba ya jin za a dawo da tattaunawar cikin gaggawa.
Ya kara da cewa: “Kafin yanke shawarar komawa kan tattaunawar, dole ne Iran ta fara tabbatar da cewa Amurka ba za ta sake kai wa kasarta harin soji ba yayin tattaunawar.”
Ya ce: Ya yi imani tare da wannan la’akari, cewa har yanzu Iran tana bukatar karin lokaci, amma kofofin diflomasiyya ba za su taba rufewa ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
Hukumomin Iran sun bayyana cewa aƙalla mutum 935 ne suka rasa rayukansu a hare-haren Isra’ila yayin yaƙin kwanaki 12 da ya gudana tsakaninsu da ƙasar.
Cikin waɗanda suka mutu sun haɗa har da mata 132 da yara 38, kamar yadda mai magana da yawun Hukumar Shari’a, Asghar Jahangir, ya bayyana a wata sanarwa a ranar Litinin, wacce kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito.
Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe HOTUNA: Sabon shugaban rikon APC APC ya jagoranci taron Majalisar GudanarwaA baya, Ma’aikatar Lafiya ta ce adadin wadanda suka mutu sakamakon hare-haren Isra’ila ya kai 606, sannan mutane 5,332 da suka jikkata.
Jahangir ya ce hare-haren Isra’ila kan gidan yari na Evin da ke Arewa maso Yammacin Tehran sun yi sanadin mutuwar mutum 79, ciki har da fursunoni da ma’aikatan gidan yari, da mazauna yankin.
Ya kara da cewa gidan yarin Evin ya zama ba zai iya aiki ba, kuma an kwashe fursunonin, yana mai kiran harin a matsayin “tauye hakkin ɗan’adam da kuma karya dokokin kasa da kasa.”
A ranar 13 ga watan Yunin nan ne yaƙi ya tsakanin Isra’ila da Iran ya barke, lokacin da Tel Aviv ta ƙaddamar da hare-haren sama kan sansanonin soja, nukiliya, da fararen hula na Iran.
Amurka ma ta kai hari kan cibiyoyin nukiliya na Fordow, Natanz, da Isfahan na Iran, wanda ya ƙara tsananta rikicin.
Tehran ta mayar da martani ta hanyar harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa kan Isra’ila, inda suka kashe aƙalla mutane 29 tare da jikkata fiye da 3,400, kamar yadda Jami’ar Hebrew ta Jerusalem ta bayyana.
Kafofin watsa labarai sun ruwaito cewa yaƙin ya tsaya sakamakon wata yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta dauki nauyi, wacce ta fara aiki a ranar 24 ga Yuni.