HausaTv:
2025-11-27@21:14:35 GMT

  Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa

Published: 29th, June 2025 GMT

Kwamandan rundunar Kudus dake karkashin IRGC Birgediya janar Isma’ila Ka’a’ni ya bayyana cewa; Iran ta samu nasara, kuma nasara ce wacce za ta dore da yardar Allah.

Birgediya janar Isma’ila Ka’a’ni wanda ya halarci jana’izar shahidan ta’addancin HKI ya bayyana cewa; Daga yanzu zuwa gaba abinda yake gabanmu shi ne ci gaba da samun nasarori.

Haka nan kuma ya ce; Idan har aka samu hadin kai, aka yi aiki tare a tsakanin al’ummar kasa, to komai zai tafi daidai.”

Birgediya janar Ka’a’ni ya kuma jinjina wa shahidai, yana mai kara da cewa; tafarkinsu zai cigaba da wanzuwa.

A lokacin yakin kwanaki 12 HKI ta rika watsa  cewa ta kashe kwamandan na rundunar Kudus, lamarin da ya tabbata fargaganda ce.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta gano harsasai 210 da aka jefar a kan babbar hanyar Zariya zuwa Funtuwa, a unguwar Dogo Itace da ke Samaru, Zariya.

Lamarin ya faru ne lokacin da DPO na Samaru tare da tawagarsa suke sintiri a kan hanyar.

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau

Jama’ar yankin ne suka kira rundunar cewar fasinjojin wata mota ƙirar Volkswagen Golf mai launin baƙi sun jefar da wata jaka, sannan suka tsere.

Da jami’an rundunar suka isa, sun tarar da jakar da aka jefar.

Bayan gudanar da bincike, sun gano harsasai 210 na ɗangon 7.56mm.

DPO ɗin yankin ya sanar da sauran jami’an rundunar da ke kan hanyar Funtuwa domin dakatar da motar amma ba a ga motar ba.

Ana zargin direban da fasinjojin motar sun lura da jami’an tsaron da ke kan hanyar, wanda hakan ya sa suka zubar da jakar.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya yi kira ga jama’a da ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai.

Ya jaddada ƙudirin rundunar na ci gaba da sintiri da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Ya kuma gargaɗi masu aikata laifi da su guji duk wani yunƙurin tayar da zaune-tsaye, inda ya ce duk wanda aka kama zai fuskanci hukunci mai tsanani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi