Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
Published: 29th, June 2025 GMT
Kwamandan rundunar Kudus dake karkashin IRGC Birgediya janar Isma’ila Ka’a’ni ya bayyana cewa; Iran ta samu nasara, kuma nasara ce wacce za ta dore da yardar Allah.
Birgediya janar Isma’ila Ka’a’ni wanda ya halarci jana’izar shahidan ta’addancin HKI ya bayyana cewa; Daga yanzu zuwa gaba abinda yake gabanmu shi ne ci gaba da samun nasarori.
Haka nan kuma ya ce; Idan har aka samu hadin kai, aka yi aiki tare a tsakanin al’ummar kasa, to komai zai tafi daidai.”
Birgediya janar Ka’a’ni ya kuma jinjina wa shahidai, yana mai kara da cewa; tafarkinsu zai cigaba da wanzuwa.
A lokacin yakin kwanaki 12 HKI ta rika watsa cewa ta kashe kwamandan na rundunar Kudus, lamarin da ya tabbata fargaganda ce.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari
Ya ce yana matuƙar daraja lokutan da suka gudanar tare.
Ya roƙi Allah ya bai wa iyalan Dantata da Dangote, Masarautar Kano, da al’ummar jihar da ƙasar baki ɗaya haƙuri da juriyar rashin wannan babban mutum.
“Allah Ya jikan shi Ya sa Aljannatul Firdaus makomarsa,” in ji Buhari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp