Za a birne Aminu Ɗantata a Madina – Iyalansa
Published: 28th, June 2025 GMT
Iyalan marigayi Alhaji Aminu Ɗantata, wanda ya rasu, sun bayyana cewa ya bar wasiyyar cewa a birne shi a Birnin Madina na ƙasar Saudiyya.
Majiyoyi daga cikin iyalansa sun bayyana cewa marigayin ya buƙaci a birne shi kusa da uwargidansa a Madina a duk lokacin da ya rasu.
Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’A gefe guda kuma, Majalisar Malamai ta Jihar Kano ta yi wa marigayin sallar Ga’ib a Masallacin Aliyu bin Abu Talib da ke unguwar Dangi.
Cikin wata sanarwa da ta fitar, majalisar ta bayyana cewa za a yi masa sallar ne duk d gawarsa na Birnin Dubai, na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.
An gudanar da sallar a cikin birnin Kano, da misalin ƙarfe 2 na rana.
Sanarwar ta buƙaci al’umma da su halarta domin yin sallar da kuma yi wa marigayin addu’o’i.
Alhaji Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekaru 94 bayan fama da rashin lafiya.
Ya rasu yana da ’ya’ya bakwai da jikoki da dama.
Babban sakatarensa, Mustapha Abdullahi Junaid, ne ya sanar da rasuwar a safiyar Asabar.
Ɗaya daga cikin attajirai mafiya arziƙi a Nahiyar Afirka, ya rasu ne a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE.)
Alhaji Aminu Ɗantata shi ne mai kamfanin mai na Express Petroleum & Gas, kuma a matsayin uba yake ga attajirin Afirka, Alhaji Aliko Ɗangote.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗantata Rashin lafiya rasuwa Saudiyya Aminu Ɗantata
এছাড়াও পড়ুন:
Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA
Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen ruwan sama mai karfi da zai iya haifar da ambaliya a jihohi 15 na Arewacin Najeriya da wasu wurare 68, a cikin kwanaki biyar masu zuwa.
Wannan gargadi ya fito ne daga Cibiyar Lura da Gargadin Ambaliya ta Kasa, karkashin Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, inda aka bukaci hukumomi da al’umma su dauki matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi.
Cibiyar ta bayyana jerin jihohi da wuraren da ambaliyar za ta iya shafa sun hada da:
Adamawa: Jimeta, Mubi, Mayo-Belwa, Wuro-Bokki, Yola, Farkumo Bauchi: Jama’a Nasarawa: Keffi Kaduna: Jaji, Kafanchan, Zaria, Birnin-Gwari Katsina: Katsina, Bindawa, Kaita Kebbi: Kamba, Kangiwa, Kalgo, Ribah, Sakaba, Saminaka, Gwandu, Jega, Bunza, Birnin Kebbi, Bagudo, Argungu Kano: Bebeji, Gwarzo, Karaye, Sumaila, Tundun-wada Niger: Rijau, Ibi, Chanchaga, Magama, Mashegu, Minna, Mokwa, New-Bussa, Sarkin Pawa, Wushishi Taraba: Duchi Jigawa: Miga, Ringim, Hadejia, Dutse Yobe: Potiskum, Dapchi, Gasma, Gashua, Jakusko Zamfara: Kaura Namoda, Maradun, Shinkafi, Bungudu, Gusau Sokoto: Sokoto, Gagawa, Gada, Goronyo, Isa, Wamakko, Silame, Makira Borno: Bama Kwara: JebbaHukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.
NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMAHukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.
Alkaluman da NEMA ta fitar sun nuna ceaw ambaliyar ta riga ta raba mutane 49,205 da muhallansu, ta lalata gidaje 10,663, da kuma gonaki 9,454 a al’ummomi daban-daban.
Jihohin da ibtila’in ya fi shafa sun hada da:
Imo (28,030), Ribas (22,345), Adamwa (12,613), Abia (11,907), Delta 8,810, Borno (8,164), Kaduna (7,334), Bayelsa (5,868) da Legas (5,793).
Sauran jihohin sun hada da Akwa Ibom (5,409), Niger (3,786), Ondo (3,735), Edo (3,234), Kogi (2,825), Sokoto (1,916), Kwara (2,663), Kano (1,446), Jigawa (1,428), Gombe (972), Anambra (925), da Babban Birnin Tarayya (1,025).
Da haka hukumar ta bukaci jama’a da hukumomi da su dauki matakan gaggawa don rage illar ambaliya da kare lafiyar jama’a.