Za a birne Aminu Ɗantata a Madina – Iyalansa
Published: 28th, June 2025 GMT
Iyalan marigayi Alhaji Aminu Ɗantata, wanda ya rasu, sun bayyana cewa ya bar wasiyyar cewa a birne shi a Birnin Madina na ƙasar Saudiyya.
Majiyoyi daga cikin iyalansa sun bayyana cewa marigayin ya buƙaci a birne shi kusa da uwargidansa a Madina a duk lokacin da ya rasu.
Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’A gefe guda kuma, Majalisar Malamai ta Jihar Kano ta yi wa marigayin sallar Ga’ib a Masallacin Aliyu bin Abu Talib da ke unguwar Dangi.
Cikin wata sanarwa da ta fitar, majalisar ta bayyana cewa za a yi masa sallar ne duk d gawarsa na Birnin Dubai, na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.
An gudanar da sallar a cikin birnin Kano, da misalin ƙarfe 2 na rana.
Sanarwar ta buƙaci al’umma da su halarta domin yin sallar da kuma yi wa marigayin addu’o’i.
Alhaji Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekaru 94 bayan fama da rashin lafiya.
Ya rasu yana da ’ya’ya bakwai da jikoki da dama.
Babban sakatarensa, Mustapha Abdullahi Junaid, ne ya sanar da rasuwar a safiyar Asabar.
Ɗaya daga cikin attajirai mafiya arziƙi a Nahiyar Afirka, ya rasu ne a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE.)
Alhaji Aminu Ɗantata shi ne mai kamfanin mai na Express Petroleum & Gas, kuma a matsayin uba yake ga attajirin Afirka, Alhaji Aliko Ɗangote.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗantata Rashin lafiya rasuwa Saudiyya Aminu Ɗantata
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Mika Wuya Ga ‘Yan Kama Karya
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Iran ba ta san mika wuya ba, kuma tana rubuta tarihin mutunci da jinin shahidanta
A jawabin da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi bayan halartar jana’izar shahidan Quds ya jaddada cewa: Iran ba ta san ma’anar mika wuya ba, yana mai fayyace cewa tarihi zai shaida cewa Iraniyawa sun zubar da jininsu tare da kin ba da kasarsu da mutuncinsu.
Araqchi ya bayyana a shafinsa na Instagram cewa: “Duk da zafi da rashi na shahidansu kwatsam, amma tunaninsu yana nan a cikin zukatan masu hankali, da kuma zukatan al’ummomi masu zuwa, kuma suna sane da yin riko da Imani da hanyarsu, kuma za su ci gaba da bin tafarkinsu.”
Ya kara da cewa: Za a iya ruguza cibiyoyi da gine-gine da kuma ababen more rayuwa duk muhimmancinsu, amma za su dawo da karfi da daukaka tare da shudewar zamani, sai dai girman al’umma yana da daraja kuma ba ya misaltuwa.