Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Published: 1st, July 2025 GMT
Wannan ya tayar da masa hankali, sai ya kira ‘yansanda da ke kusa da wajen.
Bayan ‘yansanda sun zo sun tono ƙasar sosai, sai suka gano wata jaririya raye tana kuka, a naɗe cikin wani yadi.
Kabiru ya ce gwamnatin ƙaramar hukumar ta ba shi damar kula da jaririyar har sai ‘yansanda sun kammala bincike.
“Na yanke shawarar kula da jaririyar ne saboda jin-ƙai da imani da ɗan Adam.
Ya ƙara da cewa za su raɗa wa jaririyar suna a ranar Laraba, kuma ya riga ya sayi rago da sauran kayayyakin buƙatar suna.
Matarsa ta ce ta ji daɗi kuma za ta karɓi jaririyar hannu biyu.
A lokacin ziyarar, Hajiya Rafa’atu Hammani, tsohuwar sakatariyar dindindin ta jihar, ta ce za ta kai rahoton lamarin ga matar gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab-Nasare Idris.
Sakataren ƙungiyar GBV, Alhaji Nasiru Idris, ya ce sun kai ziyarar ne domin nuna gode wa Kabiru saboda ceton rayuwar jaririyar, da kuma gode wa Allah.
Ya kuma yaba wa ‘yansanda saboda saurin ɗaukar mataki, tare da alƙawarin cewa za su ci gaba da tallafa wa jaririyar.
Tawagar ta bai wa jaririyar kayayyaki kamar su sabulai, kayan jarirai, madarar jarirai, katifa, gado, da kuma gidan sauro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Jaririya
এছাড়াও পড়ুন:
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp