Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Published: 30th, June 2025 GMT
Kasar Sin ta kawo karshen aikin bayar da agajin gaggawa mafi girma a gundumar Rongjiang da ke lardin Guizhou, a yankin kudu maso yammacin kasar da misalin karfe 10 na safiyar ranar Lahadi, yayin da aka kammala ruwan saman da aka tafka kamar da bakin kwarya kamar yadda mahukuntan yankin suka bayyana.
Lardin Guizhou da wasu larduna masu iyaka da shi da ke kudu maso yammacin kasar Sin sun fuskanci mamakon ruwan sama tun daga ranar 18 ga watan Yuni, lamarin da ya haifar da mummunar ambaliyar ruwa, inda lamarin ya fi muni a yankin Rongjiang.
Mahukuntan yankin sun raba yankin zuwa kashi bakwai a matsayin wadanda ambaliyar ta fi shafa tare da kwashe mazauna zuwa wasu manyan wurare masu tudu. An kwashe fiye da mutane 40,000 zuwa wurare masu aminci tun karfe 6 na yammacin ranar Asabar saboda rigakafin hadarin ambaliyar.
Kasar Sin ta ware karin kudi yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.96 daga cikin kasafin kudin gwamnatin tsakiya don tallafa wa ayyukan ba da agajin gaggawa da farfado da lardin Guizhou da ambaliyar ruwan ta shafa, inda hakan ya kara adadin kudin da aka ware zuwa yuan miliyan 200, kamar yadda hukumar raya kasa da gudanar da gyare-gyare ta kasar ta bayyana. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi
Tsohon Gwamnan Anambra, Peter Obi ya ce zai yi takarar shugabancin Nijeriya a 2027 domin ba zai shiga duk wata yarjejeniyar haɗakar takara da kowa ba.
Obi wanda ya yi takarar shugabancin Nijeriya a Zaben 2023 a karkashin inuwar jam’iyyar Labour (LP), ya tabbatar wa magoya bayansa cewa babu gudu babu ja da baya dangane da takararsa a babban zaɓen kasar na gaba.
An sanya dokar hana fita a Kaduna An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa TalataSai dai ya ce idan har akwai wata yarjejeniya da zai kulla, ba za ta wuce wacce za ta ba shi damar zama shugaban ƙasa na wa’adi daya ba, sannan ya miƙa wa shugaba na gaba mulki a ranar 28 ga watan Mayun 2031.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya fitar, Obi ya bayyana hakan a yayin amsa tambayoyin magoya bayansa wata hira ta kai tsaye da aka yi da shi a shafin X a ranar Lahadi.
Obi ya musanta kulla yarjejeniyar tsayawa takara a karkashin tikiti daya da tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar.
Haka kuma, Obi ya ce duk wata haɗaka da za a yi wadda ba ta da kudirin kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihohin Benuwe da Zamfara…da kuma bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, to kuwa babu shi babu ita.
Kazalika, Obi ya ce yana goyon bayan tsarin da zai bayar da damar a rika karɓa-karɓar mulki a tsakanin Kudu da Arewacin Nijeriya.