Aminiya:
2025-06-30@20:35:12 GMT

APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje

Published: 30th, June 2025 GMT

Jam’iyyar APC mai mulki a Nijeriya ta tsayar da 24 ga watan Yulin bana a matsayin ranar da za ta gudanar da taronta na Majalisar Zartarwa.

Mataimakin Sakataren jam’iyyar, Barista Fetus Fuanter ne ya tabbatar wa manema labarai hakan a yau Litinin a Abuja.

Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe Jami’an tsaro sun hana taron kwamitin amintattun PDP

Fuanter ya ce kusoshin jam’iyyar za su gana kafin gudanar da taron Majalisar Zartarwar.

Taron da za a gudanar shi ne na biyu ta fuskar girma a cikin jerin tarukan da jam’iyya ke zaman yanke shawara da daukar wasu muhimman matakai bayan babban taronta na kasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba cece-kuce tun bayan murabus ɗin shugaban jam’iyyar na ƙasa ya yi a makon jiya.

A makon da ya gabata ne shugaban jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar, Abdullahi Ganduje, ya ajiye mulki a wani abu da masana ke cewa na da alaƙa da lisaafin da manyan ’yan siyasar ke yi gabanin Zaɓen 2027.

APC ta ce tuni Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ali Bukar Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaba na riƙo kafin kwamatin zaɓaɓɓu su gana game da batun.

Jami’in yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa babban dalilin da Ganduje ya bayar game da murabus ɗin nasa shi ne batun ƙoshin lafiyarsa.

Sai dai wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ta umarce shi da yin hakan.

Da ma tun lokacin aka bai wa Ganduje shugabancin jam’iyyar wasu ‘yan jam’iyyar, musamman daga yankin Arewa maso Gabas, suka riƙa gunaguni cewa su ya kamata a bai wa.

Zuwa yanzu babu tabbas game da wanda fadar shugaban ke son ya karɓi shugabancin jam’iyyar.

Daga cikin waɗanda ake raɗe-raɗin za su maye gurbin Ganduje akwai tsohon Gwamnan Nasarawa, Umar Tanko Al-Makura da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Majalisar Zartarwa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban majalisar dokokin jama’ar kasar Mexico Sergio Carlos Gutiérrez, ya bayyana yayin da wakilin babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG ya zanta da shi a kwanakin baya cewa, tunanin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama da shugaba Xi Jinping ya gabatar ya burge shi matuka.

Ya ce, an gabatar da tunanin don tattauna yadda sassan kasa da kasa za su zauna tare, da taimakawa juna, da amincewa da bambance-bambance a fannonin tattalin arziki, da yawan mutane, da yankunan kasa a tsakanin kasashen duniya, da sa kaimi ga maida bambance-bambance su zama hanyar dinkewa da juna, da kuma samar da kyakkyawan yanayin zaman rayuwar al’ummun kasa da kasa. Kana yana fatan jama’ar kasashen duniya ciki har da ta Sin da ta Mexico, za su ji dadin zaman rayuwa mai inganci.

Ban da wannan kuma, Gutiérrez ya yi nuni da cewa, Sin da kasashen Latin Amurka sun taimakawa juna, da more fasahohin samun ci gaban juna, da sa kaimi ga samun zaman rayuwar jama’a mai inganci, kana bangarorin biyu sun yi kokarin samar da yanayin zaman rayuwa mai tsaro, da inganci ga jama’arsu.

Ya ce, bisa yanayin da ake ciki a duniya, zurfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, zai jagoranci Sin da kasashen Latin Amurka, ga bin hanyar samar da zaman rayuwa mai inganci ga al’umma. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce; Dokar Majalisar Shawarar Musulunci Ta Kasar Kan Hukumar IAEA Dole Ne Aiki Da Ita
  • Iran Ta Bukaci Gudanar Da Bincike Kan Dalilin Isra’ila Na Kai Harin Kan Gidan Yarin Tehran
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  • Ganduje: Dalori ya kira taron Majalisar Gudanarwar Jam’iyyar APC
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  • Yau za a yi Jana’izar Aminu Dantata a Madina
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  • Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Jaddada Cewa: Iran Tana Da Hakkin Tace Sinadarin Uranium A Kasarta