Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi
Published: 30th, June 2025 GMT
‘Yan sandan Tehran sun sanar da kama wani dan leken asirin kungiyar leken asirin Isra’ila ta “Mosad” a cikin daya daga tasoshin jiragen kasa na birnin Tehran.
Dan leken asirin wanda aka watsa furucin da ya yi, ya bayyana cewa aikinsa shi ne kera jiragen sama marasa matuki da kuma ‘yan kananan jirage, a yammacin Tehran bisa umarnin wadanda su ka dauke shi aiki masu alaka da Mosad.
Haka nan kuma ya ce, ya tattara bayanai akan wasu muhimman wurare da cibiyoyi,musamman wadanda su ka shafi yadda naurorin kariyar samaniyar saman Iran suke aiki, tare da aikewa da su zuwa kasashen waje.
Majiyar ‘yan sandan ta ce, an kama mutumin ne bayan da aka dade ana bin diddiginsa da kuma tantance ayyukan da yake yi,da hakan ya taimaka wajen dakile wasu hare-hare.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Titunan Birnin Tehran Sun Cika Makil Da Masu Jana’izar Shahidan Ta’addancin HKI
Kamfanin Dillancin Labarun “Mehr” ya nakalto cewa; Tun da jijjfin safiyar yau Asabar ne tasoshin jiragen kasa da na safa-safa su ka cika makil da masu son halarta babban filin Juyi na Tehran da can ne zai zama masonin rakiyar shahidan zuwa makwancinsu na karshe.
Ana iya ganin dubun dubatar mutane da su ka fito daga kowane bangare na al’ummar Iran domin halartar jana’izar ,yara, mata, masana da kwamandojin soja, wacce ta fara da misalin karfe 8;00 na safiyar yau agogon Tehran.
Adadin shahidan da ake jana’izar tasu a yau, sun kai 60, za kuma a rufe su ne a makabartar “Baheshti-Zahra” wacce take kunshe da shahidan juyin juya halin musulunci.
A shirnmu na rana za a ji cikakken bayani akan yadda jana’izar ta kasance.