HausaTv:
2025-08-16@09:06:03 GMT

Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya

Published: 1st, July 2025 GMT

Magajin garin birnin Tehran ya bayyana cewa: Karyar ‘yan sahayoniyya ya tonu na cewa ba su kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran ba

Magajin garin birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran Ali-Ridha Zakani ya tabbatar da cewa: Karairayi da ‘yan sahayoniyya suke yadawa dangane da rashin kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran a fili yake karara.

Yana mai nuni da cewa akwai kwarararn dalilai da ake da su wadanda suke fallasa karyar wadannan ikirari.

A cikin bayanansa, Zakani ya ce: Dalilai kan wadannan karairayi su ne kaburbura gawawwaki da suka hada da fili mai lamba ta 42 a makabartar Al-Jannar – Zahra da ke babban birnin Tehran. Ya bayyana cewa, duk wanda ya ga jerin sunayen wadanda suka yi shahada a lokacin yakin zai iya ganin karara irin karyar da ‘yan sahayoniyya suka shirga, kamar yadda kowa zai iya ganin gine-ginen da aka kai musu hare-hare a birnin Tehran.

Zakani ya kuma yi ishara da hare-haren baya- bayan nan da yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya suka kai kan wuraren fararen hula da suka hada da cibiyoyin kiwon lafiya, inda ya kara da cewa, gwamnatin ‘yan sahayoniyya sun kai hare-hare kan motocin daukar marasa lafiya da asibitoci da ba su bukatar wata shaida wajen tabbatar da karairayin ‘yan sahayoniyya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan sahayoniyya birnin Tehran

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Wani mazaunin Safana, Iliyasu Sani, ya ce sulhun ya kawo sauƙi ga rayuwar jama’a, domin yanzu suna iya zuwa kasuwa da yin noma ba tare da fargaba ba.

Masani a fannin tsaro, Kabiru Adamu, ya ce talauci da rashin tsaro ne suka sa jama’a neman mafita da kansu.

Ya kuma bayyana cewa idan duk ɓangarorin suka tsaya kan alƙawarin da aka yi, wannan sulhu na iya zama mataki na farko na samun zaman lafiya na dindindin a yankin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Ansarullahi Ta Kasar Yemen Ya Ce; Yahudawan Sahayoniyya Suna Yakar Al’ummar Falasdinu Duka Ne
  • An Bukaci Ficewar Marasa Lafiya da Likitoci daga Wani Babban Asbiti A birnin London
  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Alhininsa Kan Kashen Masanan Kasar Iran Da ‘Yan Sahayoniyya Suka Yi
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida