HausaTv:
2025-07-02@02:23:48 GMT

Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya

Published: 1st, July 2025 GMT

Magajin garin birnin Tehran ya bayyana cewa: Karyar ‘yan sahayoniyya ya tonu na cewa ba su kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran ba

Magajin garin birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran Ali-Ridha Zakani ya tabbatar da cewa: Karairayi da ‘yan sahayoniyya suke yadawa dangane da rashin kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran a fili yake karara.

Yana mai nuni da cewa akwai kwarararn dalilai da ake da su wadanda suke fallasa karyar wadannan ikirari.

A cikin bayanansa, Zakani ya ce: Dalilai kan wadannan karairayi su ne kaburbura gawawwaki da suka hada da fili mai lamba ta 42 a makabartar Al-Jannar – Zahra da ke babban birnin Tehran. Ya bayyana cewa, duk wanda ya ga jerin sunayen wadanda suka yi shahada a lokacin yakin zai iya ganin karara irin karyar da ‘yan sahayoniyya suka shirga, kamar yadda kowa zai iya ganin gine-ginen da aka kai musu hare-hare a birnin Tehran.

Zakani ya kuma yi ishara da hare-haren baya- bayan nan da yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya suka kai kan wuraren fararen hula da suka hada da cibiyoyin kiwon lafiya, inda ya kara da cewa, gwamnatin ‘yan sahayoniyya sun kai hare-hare kan motocin daukar marasa lafiya da asibitoci da ba su bukatar wata shaida wajen tabbatar da karairayin ‘yan sahayoniyya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan sahayoniyya birnin Tehran

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bukaci Gudanar Da Bincike Kan Dalilin Isra’ila Na Kai Harin Kan Gidan Yarin Tehran

Iran ta bukaci gudanar da binciken gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai gidan kurkukun Evin

A cikin wata wasika da ya aike wa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniyar, jakada kuma zaunannen wakilin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya, Amir Sa’ed Irawani, ya yi kira da a gaggauta gudanar da bincike mai tsanani kan harin da ‘yan sahayoniyya suka kai gidan yarin Evin da ke birnin Tehran.

A cikin wasikar, Irawani ya rubuta cewa: Wannan harin da aka kai a ranar Litinin, 23 ga watan Yunin wannan shekara ta 2025, an nufi wani gidan yarin farar hula da gangan, wanda hakan ya sabawa dokokin kare hakkin dan Adam na kasa da kasa da kuma muhimman ka’idojin Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya.

A yayin da yake yin Allah wadai da harin, jakadan kasar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Bisa la’akari da irin hadari da kuma munin wannan mugun aiki da aka aikata, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bukaci kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da babban sakataren Majalisar da su yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai wa gidan yarin Evin. Ba tare da wata shakka ba, harin yana matsayin babban cin zarafi ga dokokin jin kai na ƙasa da ƙasa da dokokin haƙƙin ɗan adam na duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Iran Ta Bukaci Gudanar Da Bincike Kan Dalilin Isra’ila Na Kai Harin Kan Gidan Yarin Tehran
  • Dalibai 29 Suka Rasu A Turmutsitsin Tserewa Ga Fashewar Taransifoma A Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan