Manjo Janar Mousawi ya bayyana cewa: Suna shakka da kokwanto kan gaskiyar tsagaita bude wuta shin za ta dore kuwa tsakaninsu da ‘yan sahayoniyya

Babban hafsan hafsoshin sojin kasar Iran ya yi gargadin gazawar yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yana mai nuni da rashin kwarin gwiwa kan kudurin makiya na cika alkawuran da suka dauka.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da ministan tsaron kasar Saudiyya Yarima Khalid bin Salman, babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Seyyed Abdurrahim Mousawi ya bayyana cewa: Harin da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan kasar Iran ya zo ne duk da kamewa da kai zuciya nesa da Iran take yi, kuma a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa ba na kai tsaye ba da Amurka.

Mousavi ya bayyana cewa: Wadannan gwamnatocin biyu sun sake tabbatar da rashin amincewarsu da duk wani tsari na kasa da kasa, kamar yadda aka nunawa duniya karara a tsawon kwanaki 12 na yakin.

Ya kara da cewa: “Ba su fara yakin ba, amma sun mayar da martani ne da dukkan karfinsu, duba da irin shakkun da suke da shi kan jajircewar da makiya suka yi, ciki har da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, amma Iran a shirye take ta kaddamar da wani muhimmin martani idan aka sake kai mata hari.”

A nasa bangaren, ministan tsaron Saudiyya Yarima Khalid bin Salman ya ce: “Ba wai kawai masarautar ta yi Allah-wadai da hare-haren ba ne, har ma ta yi kokarin kawo karshen yakin wuce gona da irin.” Haka nan kuma ya mika ta’aziyyarsa ga shahadar wasu kwamandojin sojojin Iran a yakin baya-bayan nan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan

Rahotannin da su ke fitowa daga kasashen biyu sun ce a jiya Asabar an yi musayar wuta a tsakanin masu tsaron kan iyaka, bisa zargin da Islamabad take yi wa Kabul da taimakon kungiyoyi masu dauke da makamai.

A can kasar Afghanistan kuwa majiyar tsaro ta ce ana yi fada da sojojin Pakistan akan iyakokin jahohi 7. Ma’aikatar tsaron Afghanistan ta ce, sun kai wa sojojin Pakistan hari akan iyakar Diyorand a matsayin mayar da martanin ta sama da Pakistan ta kai wa birnin Kabul da jahohin Khust da Nangarhar.

Pakistan tana zargin kungitar Taliban ta kasarta da kai hari daga cikin kasar Afghanistan,lamarin da Kabul take korewa.

Harin da kungiyar Taliban din Pakistan a yankin Kahibar dake kan iyaka, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 23 daga cikinsu da akwai jami’an tsaro 20 da kuma fararen hula 3.

Bayanin rundunar sojan kasar Pakistan y ace; Hare-haren da kungiyar ta Taliban take kai wa sun ci rayukan mutane fiye da 500 daga cikinsu da akwai sojoji 311 da ‘yan sanda 73.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza
  • Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba
  • Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan
  • Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta
  • Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref
  • HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza