Manjo Janar Mousawi ya bayyana cewa: Suna shakka da kokwanto kan gaskiyar tsagaita bude wuta shin za ta dore kuwa tsakaninsu da ‘yan sahayoniyya

Babban hafsan hafsoshin sojin kasar Iran ya yi gargadin gazawar yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yana mai nuni da rashin kwarin gwiwa kan kudurin makiya na cika alkawuran da suka dauka.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da ministan tsaron kasar Saudiyya Yarima Khalid bin Salman, babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Seyyed Abdurrahim Mousawi ya bayyana cewa: Harin da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan kasar Iran ya zo ne duk da kamewa da kai zuciya nesa da Iran take yi, kuma a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa ba na kai tsaye ba da Amurka.

Mousavi ya bayyana cewa: Wadannan gwamnatocin biyu sun sake tabbatar da rashin amincewarsu da duk wani tsari na kasa da kasa, kamar yadda aka nunawa duniya karara a tsawon kwanaki 12 na yakin.

Ya kara da cewa: “Ba su fara yakin ba, amma sun mayar da martani ne da dukkan karfinsu, duba da irin shakkun da suke da shi kan jajircewar da makiya suka yi, ciki har da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, amma Iran a shirye take ta kaddamar da wani muhimmin martani idan aka sake kai mata hari.”

A nasa bangaren, ministan tsaron Saudiyya Yarima Khalid bin Salman ya ce: “Ba wai kawai masarautar ta yi Allah-wadai da hare-haren ba ne, har ma ta yi kokarin kawo karshen yakin wuce gona da irin.” Haka nan kuma ya mika ta’aziyyarsa ga shahadar wasu kwamandojin sojojin Iran a yakin baya-bayan nan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da gagarumin jana’izar tare da karramawq ga kwamandojinta da masana kimiyyar nukiliya da wasu ’yan kasar da Isra’ila ta kashe a yankin kwana 12 da aka gwabza a tsakanin ƙasashen.

Iran ta shirya gagarumin jana’izar a ƙwaryar birnin Tehran kwana huɗu bayan Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da ɓangarorin biyu ke iƙirarin nasara a yaƙin da aka fara ranar 13 ga Yuni, 2025.

A safiyar Asabar daruruwan dubban mutane ne suka fito ɗauke da tutocin ƙasar suna wake-waken jinjina domin karrama kwamandojin da suka kwanta dama a wurin jana’izar.

Mutanen sun kuma riƙa daga hotunan mamatan a matsayin waɗanda suka yi mutuwar shahada, a yayin da suke la’antar Isra’ila da Amurka.

Daga cikin kwamandojin da Isra’ila ta kashen har da jagoran Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran Janar Hossein Salami da Janar Amir Ali Hajizadeh da wani ƙwararren masanin kimiyyar makamashin nukiliya, Mohammad Mehdi Tehranchi.

Za a iya tuna cewa Amurka ta kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran hare-hare a ƙarshen makon da ya gabata, kafin daga bisani a tsagaita wuta.

Amurka da Isra’ila sun yi iƙirarin cewa hare-haren sun yi gagarumar nasarar ruguza shirin kera makaman nukiliya na Iran.

Amma daga bisani Iran ta ƙaryata su, da cewa babu wata illa da hare-haren suka yi wa shirinta da makamashin nukiliya.

A ranar Talata Shugaban addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya karyata abin da ya kira kambama harin da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi na cewa harin hare-haren sun mayar da shirin nukiliyar Iran baya da shekaru.

An kashe manyan sojojin da masa kimiyyar nukiliyar Iran ne a harin da Isra’ila ta fara kaiwa bisa hujjar neman daƙile shirin Iran na mallakar makamin nukiliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Yin Kutse Cikin Yankunan Kasar Siriya
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe
  • An Bude Juyayin Ashura A Fadin Iran
  • An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
  • Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja