Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
Published: 2nd, July 2025 GMT
Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran ta jaddada cewa: Gudanar da masana’antun nukiliyar kasar za ta ci gaba da kuma fadada bunkasar da suke samu
Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran, Mohammad Islami, dangane da yadda yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran, ya jaddada cewa: Masana’antar nukiliya ba wani abu ba ne da za a iya rusa shi ta hanyar jefa masa bam saboda fasahar masana’antar nukiliya irin ta Iran tana bunkasa ce da ilimummukan masana ‘yan asalin kasa da suke da zurfin fasahar ilimin.
Kamfanin dillancin labaran Mehr ya watsa rahoton cewa: Mohammad Islami shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran ya bayyana cewa, bayan wani taron majalisar ministocin kasar da aka gudanar a ranar Laraba, don tattaunawa kan yadda gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka kai harin wuce gona da iri kan cibiyoyin nukiliyar kasar Iran, cewa: Wannan farmakin da aka kai kan Iran, wani rauni ne ga kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya da kuma nuna cewa dokar daji ta mamaye duniya, kuma wadanda ba su da karfi ba za su iya ci gaba da rayuwarsu ba lamarin da tuni al’ummar Iran suka fahimci hakan da kyau.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Nukiliya ta Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa Alhaji Aminu Zakari, yace ziyarar kwamatin a kananan hukumomin jihar 27 tana bada damar ganawa kai tsaye a tsakanin masu ruwa da tsaki domin karfafa dabi’ar aiki tare da juna da kuma kyautata alaka a tsakanin bangarori daban daban.
Ya yi wannan tsokaci ne lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin ziyarar aiki a sakatariyar karamar hukumar Gwiwa.
Yace a lokacin irin wannan ziyarar, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi domin tabbatar da gudanar harkokin kananan hukumomi kamar yadda ya kamata, ta hanyar aiki da tanade-tanade da kuma ka’idojin kashe kudade.
Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar Kwamatin yana kafa kananan kwamitoci domin ziyarar gani da ido dan tantance ayyukan raya kasa a lungu da sakon karamar hukumar domin tabbatar da cin moriyar kashe kudaden gwamnati ta hanyar ayyuka masu inganci.
A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwiwa, Malam Muhammad Abubakar Zakari, ya bayyana kwarin gwiwar cewa ziyarar kwamatin za ta zaburar da shugabanni wajen kashe kudade ta hanyar da ta dace, tare da wanzar da shugabanci nagari.
Malam Muhammad Zakari ya kuma sha alwashin bada cikakken hadin kai da goyon baya domin samun nasarar ziyarar.
Kazalika, ya bada tabbacin amfani da shawarwarin kwamatin domin ci gaban karamar hukumar sa.
Sauran ‘Yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama, Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin Malam Madori Alhaji Hamza Adamu Ibrahim Babayaro da sakataren Kwamatin da mataimakan sa da Oditoci biyu.
Usman Mohammed Zaria