Aminiya:
2025-10-13@17:12:17 GMT

Za a tono gawar tsohon Gwamna Alao-Akala domin gwajin jinin ’ya’yansa

Published: 28th, June 2025 GMT

Ana neman tono gawar tsohon Gwamnan Jihar Oyo, marigayi Otunba Christopher Adebayo Alao-Akala, domin yin gwajin jini (DNA) da nufin tantance halastattun ’ya’yansa da za su ci gadon dukiyar da ya bari.

Batun tono gawar ta kunno kai ne bayan taƙaddama ta yi tsami a tsakanin ’ya’yan tsohon gwamnan a kan rabon gadonsa.

Babbar ’yar marigayin mai suna Uwargida Oluwatoyin Alao-Aderinto ce ta shigar da ƙara a gaban Mai Shari’a Taiwo na Babbar Kotun Jihar Oyo ta hannun lauyanta, Oladipo Olasope (SAN), inda ta roƙi kotun ta bayar da umarnin tono gawar mahaifin nasu daga kabarinsa domin yin gwajin ƙwayar halittarsa ga wasu mutane bakwai da ke iƙirarin cewa su ne halastattun ’ya’yan marigayin.

Uwargida Aderinto ta shigar da ƙarar ne bayan abin da ta kira barazanar da ’yan uwanta ke yi na neman cire sunanta daga cikin jerin halastattun ’ya’yan marigayin da za su gaje shi.

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja

A takardar ƙarar, ta bayyana cewa ɗaukar matakin tono gawar mahaifin nasu da yin gwajin jini ga ’yan uwan nata su bakwai, har da ita kanta, shi ne zai taimaka wajen tantance ainihin halastattun ’ya’yan

marigayin da suka cancanci cin gadon ɗimbin dukiyar da ya bari a ciki da wajen Nijeriya.

Tsohon Gwamna Otunba Adebayo-Alao Akala ya mutu ne cikin watan Janairu na shekarar 2022, inda aka binne shi a cikin watan Oktoban shekarar a wani ƙasaitaccen kabari da aka gina a harabar gidansa da ke mahaifarsa a garin Ogbomosho da ke jihar.

Dukiyoyin da tsohon gwamnan ya mutu ya bari da ’ya’yan nasa suke jayayya a kai, waɗanda Lauya Oladipo ya gabatar gaban kotun, sun haɗa da rukunin gidajen alfarma a biranen Ibadan da Legas da Abuja da kuma ƙasashen Amurka da Birtaniya da wani katafaren otel a ƙasar Ghana.

Sauran sun haɗa da motocin alfarma da maƙudan kuɗaɗe a bankuna daban-daban a Nijeriya da ƙasashen Amurka da Birtaniya.

Tushen rikicin rabon gadon Alao-Akala

An fara wannan taƙaddama a tsakanin ’ya’yan tsohon gwamnan ne bayan da aka binne gawarsa a watan Oktoba na shekarar 2022.

Rikicin ya samo asali ne bayan mutum biyu daga cikin ’ya’yannsa masu suna Kemi Alao-Akala da Olamide Alabi suka samu izinin daga magatakardan kotun rabon gado na Jihar Oyo, ba tare da sani ko amincewar Uwargida Oluwatoyin Alao-Aderinto ba, a matsayinta na babbar ’ya ga marigayin.

Ta yi zargin cewa ’yan uwan nata sun kitsa lamarin ne da gangan ta bayan fage, kuma abin da suka yi ya saɓa wa dokokin rabon gado na Nijeriya. Don haka ta zargi ’yan uwan nata da neman yin kwanciyar magirbi a kan dukiyar da mahaifinsu ya bari.

A watan Agustan2023, Lauya Oladipo Olasope (SAN) ya yi zargi a cikin wata wasiƙa cewa, ƙoƙarin cire sunan Uwargida Oluwatoyin AlaoAderinto, a matsayinta na babbar ’yar Marigayi Adebayo Alao-Akala daga cikin jerin ’ya’yansa zai iya haifar da babbar ɓaraka da rabuwar kawunan wannan babban gida. Saboda haka ya nemi kotun ta hanzarta ɗaukar matakin biyan buƙatun wadda yake karewa, na tono gawar marigayin domin a kawo ƙarshen matsalar ɗungurungum.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adebayo Alao Akala dukiya gwajin jini Tono gawa

এছাড়াও পড়ুন:

Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref

Mataimakin shugaban kasar Iran Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa, batun kifar da gwamnatin JMI bayan yakin kwanaki 12 ya kuma fita daga abinda makiya zasu iya.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar yanakalto mataimakin shugaban kasa na farko yana fadar haka a ranar Alhamis da ta gabata, ya kuma kara da cewa a cikin yakin kwanaki 12 wanda kasashen Amurka da HKI suka dorawa kasar sun so su kifar da gwamnatin JMI a cikin kwanaki 3 zuwa 4 amma suka kasa.

Ya ce hatta babban sakataren MDD Antonio Guterres ya tabbatar da haka a wata tattaunawa da shi dangane daha. Ya kuma tabbatar da cewa makiyan JMI ba zasu iya tumbuke tsarin ba.

Yasashen yamma musamman Amurka suna kokarin kifar da JMI tun bayan kafata a shekara 1979, amma duk kokarin da suke yi yana lalacewa bay a kaiwa ga natija. Hatta yakin kai tsaye da suka dorawa kasar a cikin watan yunin da ya gabata ya kaisa kaiwa ga manufarsu.

Aref yace a duk lokacinda suka su kifar da gwamnatin Iran sai kara karfe take, kuma mutanen kasar suna kara samun hadin kai.

Ya ce, mu ba maso takalar yaki bane, amma duk lokacinda aka dora mana yaki makiya ne suke neman a dakatar da abinda suka fara.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta October 11, 2025 Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref