Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Published: 29th, June 2025 GMT
Bisa ga sanarwar, wannan wani sashe ne na sabon yunkuri na ba da cikakken ‘yanci ga majalisar kananan hukumomi 774 na kasar nan.
Haka kuma a kan gyaran kananan hukumomi, wata kudirin doka da ke neman kirkiro wata hukumar zabe mai zaman kanta ta kananan hukumomi (NALGEC), wanda za ta dunga shiryawa, gudanar da kuma kula da zaben kananan hukumomin, za a kuma gabatar da ita ga ‘yan Nijeriya don yin nazari a taron sauraron jin ra’ayoyin.
Wadansu batutuwa da aka fitar a cikin sanarwar da suka hada da kudirin dokoki guda biyu kan tsaro da manufar samar da ‘yansandan jihohi da majalisar tsaro na jihohi don tsara manufofin tsaro na cikin gida a matakin yankuna.
“A bangaren gyaran manufifin kudade kuwa, za a duba dokoki guda shida ciki har da dokar da za ta ba da iko ga hukumar rarraba haraji ta kasa don tilasta bin doka da rarraba kudaden haraji daga asusun gwamnatin tarayya da kuma inganta tsarin nazarin hanyar rarraba kudaden.
“A cikin wata sabuwar mataki tare da magance rashin daidaiton jinsi, kwamitin zai kuma yi nazarin wata doka da za ta samar da karin kujeru ga mata a cikin majalisun tarayya da majalisun jihohi.
“Don karfafa masarautun gargajiya, za a duba wani kudirin doka za sauya kundin tsarin mulki domin kafa majalisar masarautu gargajiya ta kasa da majalisar masarautun gargajiya ta jihohi da majalisar masarautun gargajiya ta kananan hukumomi.
“A kan gyaran tsarin zabe kuwa, za a tattauna wani shawarwari da ke neman gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 don ba da damar tsayawa takara kai tsaye a kowane mataki na zabe, daga kananan hukumomi zuwa shugabancin kasa a taron sauraron jin ra’ayoyin.
“Jimlar wasu kudirorin doka fiye da 20 da ke neman gyara tsarin shari’a na kasar, ciki har da lokacin da ake zartar da hukunci da kuma fadada ikon kotunan zabe, suna daga cikin batutun da za a duba.
“Shawarwari guda talatin da daya kan kirkiro jihohi, suna cikin batutun da za a dubawa a taron sauraron jin ra’ayoyin.”
Kwamitin ya jaddada muhimmancin shigar jama’a wajen tsara kundin tsarin mulkin kasar, ya yi kira ga kowa da ya halarci taron sauraron jin ra’ayin jama’a na yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Gyaran sauraron jin ra ayoyin taron sauraron jin ra
এছাড়াও পড়ুন:
Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce talauci da nuna bambanci na daga cikin manyan dalilan da ke hana yara mata damar samun ilimi a jihar.
Ta bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Yara Mata ’Yan Makaranta ta Duniya ta shekarar 2025, wanda Shirin AGILE tare da Access Initiative Africa da Nudge Initiative suka shirya a Gombe.
Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a BornoA wajen bikin, Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Asma’u Inuwa Yahaya, ta yaba da yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tabbatar da cewa ba a bar wata yarinya a baya wajen samun ilimi.
Ta ce Gwamnan jihar, ya bai wa ilimin yara mata muhimmanci, wanda hakan ya sa ake samu ƙaruwa yara mata da ke zuwa makaranta.
Kwamishiniyar, ta ƙara da cewa ma’aikatar ilimi tana aiki wajen samar da sabbin manufofi da tsare-tsare da za su taimaka wajen rage waɗannan matsaloli da tabbatar da damar ilimi ga kowa cikin adalci.
A nata jawabin, Kodinetan Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce bikin na bana an shirya shi ne don ƙarfafa gwiwar yara mata wajen ci gaba da neman ilimi duk da ƙalubalen da suke fuskanta.
Ta gode wa Uwargidan Gwamnan da ma’aikatar ilimi bisa goyon bayansu.
Haka kuma, Akawun Majalisar Dokokin Jihar Gombe, Barista Rukayyatu Jalo, ta shawarci yara mata da su dage wajen yin karatu, inda ta bayyana cewa ilimi ne hanyar da za ta gina rayuwarsa.
Wasu daga cikin ɗaliban da suka halarci bikin, sun bayyana farin ciki da godiya kan shirya taron saboda yadda ya ƙara musu ƙwarin gwiwa.
Ɗalibai da dama sun gudanar da muhawara da wasan kwaikwayo a wajen taron.