Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
Published: 30th, June 2025 GMT
Bayan hare-haren da kungiyoyin yan ta’adda masu iko da kasar Siriya suka kai kan wani Cuci a kasar Siriya jami’an gwamnatin kasar Siriya sun nuna damuwarsu da yiyuwar wadannan kungiyoyi su kawo hare-hare a cikin kasar ta Lebanon musamman a cikin wadan nan kwanaki na makokin Imam Hussain (a).
Wani Jami’in gwamnati a kasar ta Lebanon ya fadawa Jaridar da The National ta kasar Amurka kan cewa a makon da ya gabata an kama wani shugaban yan kungiyar yan ta’adda ta ISIS a cikin kasar, tare da zarginsa da shiri hare-hare masu yawa a kasar Lebanon.
Kafin haka dai a cikin watan da ya gabata wani dan ta’ada ya tarwatsa kansa a cikin wani coci a birnin Damascus babban birnin kasar Siriya inda ya kashe mutane 25.
Kungiyar yan ta’adda ta Daesh dai sun fara aiki karkashin kasa tun bayan da dakarun kungiyar Hizbulla.. da kuma sojojin kasar Lebanon sun fatattakesu a shekara 2017. Sannan a wasu lokutan sun kai hare-hare kan kungiyar Hizbullah a kasar.
Sannan bayan kungiyar HTS ta kwace mulki a hannun shugaba Asad a shekarar da ta gabata, har yanzun akwai yiyuwar barazanar hare-haren ISIS tana nan a kan kasar ta Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Siriya yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba
Ya kuma ce matakan takaita fitar da ma’adanan farin karfe da Sin ta dauka a baya bayan nan, ba su da alaka da kasar Pakistan. Yana cewa matakai ne da gwamnatin Sin ta dauka bisa doka da oda da nufin inganta tsarinta na fitar da kayayyaki. (Fa’iza Mustapha)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA