Aminiya:
2025-07-01@14:37:10 GMT

Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli

Published: 1st, July 2025 GMT

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 22 ga watan Yulin wannan shekara domin sauraron bukatar ba da belin da Tukur Mamu, da ake zargi da daukar nauyin ta’addanci Mai shari’a Mohammed Umar ya tsayar da ranar ne biyo bayan dage shari’ar da lauyan Manu, Johnson Usman, SAN, ya nema, domin ba shi damar yin nazari tare da ba da amsa da ya dace kan karar da lauyan gwamnatin tarayya, David Kaswe ya shigar a kansa.

A cikin bukatar da Mamu ya gabatar a jiya Litinin 30 ga watan Mayu, ya nemi a bayar da belinsa dsaboda yanayin rashin lafiyarsa. Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya Ya nemi Gwamnatin Tarayya ta ba shi izini a kai shi asibiti don yin aikin tiyata kamar yadda likitoci a kasar Masar da na Najeriya suka ba da shawarar. Tun a ranar 21 ga Maris na shekarar 2023 ne dai gwamnatin tarayya ta gurfanar da Mamu a gaban kuliya bisa zarginsa da taimakawa ta’addanci a kasar nan. Ana masa tuhume-tuhume guda 10 da ke da alaka da ta’addanci amma ya musanta duka zarge-zargen.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

Gabanin fara wasannin ƙasashen Afrika na ƙwallon ƙafa ta mata da hukumar ƙwallon ƙafa ta nahiyar Afirka (CAF) ta shirya a ƙasar Morocco da za a fara a ranar Asabar, Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF) za ta ƙaddamar da sabon kofin gasar a wani ɓangare na ƙoƙarin ɗaukaka wasan ƙwallon ƙafa na mata a nahiyar Afrika.

A ranar Laraba, 02 ga watan Yuli na shekarar 2025 za a ƙaddamar da sabon kofin gasar cin kofin Afrika ta mata a ƙasar Morocco, ƙasar da za ta karɓi baƙuncin gasar ta bana, sabon kofin wani ɓangaren ne na burin shugaban CAF Dr Patrice Motsepe na bunƙasa ƙwallon ƙafa na mata a Afrika.

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

CAF za ta ƙaddamar da kofin a shafukanta na sada zumunta sannan kuma a wani taron da ta shirya gudanarwa tare da masu ɗaukar nauyin gasar ta bana, a ranar Asabar 05 ga Yuli, 2025 za a fara gasar cin kofin Afrika ta mata, a filin wasa na Olympic da ke Rabat yayinda da masu masaukin baƙi, Morocco za ta karawa da Zambia.

Ranar Lahadi 6 ga watan Yuli Nijeriya za ta kece raini da ƙasar Tunisia a wasan rukunin B a filin wasa na Larbi Zaouli dake birnin Casablanca na ƙasar Moroko da misalin karfe 4 na yamma Agogon Nijeriya a ƙarƙashin jagorancin koci Justin Madugu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  • CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
  • Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
  • Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
  • Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
  • Monaco ta dauki Paul Pogba