Aminiya:
2025-08-16@01:00:27 GMT

Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli

Published: 1st, July 2025 GMT

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 22 ga watan Yulin wannan shekara domin sauraron bukatar ba da belin da Tukur Mamu, da ake zargi da daukar nauyin ta’addanci Mai shari’a Mohammed Umar ya tsayar da ranar ne biyo bayan dage shari’ar da lauyan Manu, Johnson Usman, SAN, ya nema, domin ba shi damar yin nazari tare da ba da amsa da ya dace kan karar da lauyan gwamnatin tarayya, David Kaswe ya shigar a kansa.

A cikin bukatar da Mamu ya gabatar a jiya Litinin 30 ga watan Mayu, ya nemi a bayar da belinsa dsaboda yanayin rashin lafiyarsa. Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya Ya nemi Gwamnatin Tarayya ta ba shi izini a kai shi asibiti don yin aikin tiyata kamar yadda likitoci a kasar Masar da na Najeriya suka ba da shawarar. Tun a ranar 21 ga Maris na shekarar 2023 ne dai gwamnatin tarayya ta gurfanar da Mamu a gaban kuliya bisa zarginsa da taimakawa ta’addanci a kasar nan. Ana masa tuhume-tuhume guda 10 da ke da alaka da ta’addanci amma ya musanta duka zarge-zargen.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda ɗaukar matasan da aka horar ƙarƙashin shirin GOSTEC aiki a matsayin cikakkun ma’aikata.

Ya ce wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnati wajen taimaka wa matasa domin rage zaman banza da kuma ba su damar dogaro da kai.

Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan Gwamnatin Gombe za ta ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13

Ya ƙara da cewa, yanzu wasu daga cikin matasan sun za su hidimata wa al’umma, saɓanin halin da suke ciki a baya.

Ya roƙi matasan su zama masu gaskiya, riƙon amana da kishin ƙasa, inda ya bayyana cewa su ne ginshiƙin ci gaban kowace al’umma.

Ɗaya daga cikin matasan da aka ɗauka aikin, Musa Abdullahi, ya ce shirin GOSTEC, ya sauya rayuwarsa daga neman aiki zuwa taimakawa wajen bunkasa tattalin arziƙin jihar.

Ita ma, Fatima Mohammed, ta bayyana farin cikinta da samun aikin gwamnati bayan samun horo a fannin shafukan Intanet, tare da yaba wa gwamnati saboda ƙoƙarin inganta rayuwar matasa.

Bikin, ya samu halartar jami’an gwamnati, ƙungiyoyin matasa, inda aka tattauna kan makomar matasa, ilimi da ci gaban tattalin arziƙi a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
  • Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Asibitin Dabbobi A Jihar Kwara
  • Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
  • Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina
  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
  • Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar