Limamin Tehran: Duniya Ce Ta Yi Yaki Da Iran
Published: 28th, June 2025 GMT
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a Tehran ya bayyana cewa; A cikin kwanaki 12 da su ka gabata duniya ce ta yi yaki da Iran.
Hujjatul Islam Wal Muslimin Abu Turabi Fard, ya fara hudubarsa da mika sakon ta’aziyyar shigowar ranakun Ashura, haka nan kuma jinjina ga shahidan jamhuriyar musulunci masu daraja da HKI ta yi wa kisan ta’addanci a tsawon kwanaki12 na yaki.
Limamin na Tehran ya kuma ce; Abubuwan da su ka faru a cikin kwanaki 12 na yaki sun bude wani sabon shafi na siyasa a cikin wannan yankin da kuma a fagen siyasar kasa da kasa.
Hari la yau limamin na Tehran ya jinjinawa jagoran juyin musulunci na Iran saboda yadda Iran a karkashin jagorancinsa ta zama cibiyar gwgawarmayar musulunci a cikin wannan yankin.
Limamin juma’ar na Tehran ya kuma kara da cewa; HKI ta kawo wa Iran hari ne a jajiberin ranar Idan Gadir bisa cikakken taimakon bayanai na asiri daga Amurka.”
Limamin ya kuma kara da cewa; Masu bin diddigin abubuwan da suke faruwa suna bayyana cewa; Makiya, sun dauki shekaru kusan 20 suna shirya wannan yakin. Shi kanshi fira ministan HKI ya yi furuci da hakan.
Hujjatul Islami Wal Muslimin Abu Turabi Fard ya kuma ce; HKI ta kawo wannan harin ne adaidai lokacin da ake tattaunawa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a Tehran ya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
Shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutum uku zuwa Majalisar Dattawa, domin tantance su a matsayin sabbin jakadan Najeriya.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne, ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Laraba.
Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a KadunaWaɗanda aka zaɓa su haɗa da Kayode Are daga Jihar Ogun, Aminu Dalhatu daga Jihar Jigawa da kuma Ayodele Oke.
Bayan karanta takardar Tinubu, Akpabio ya ce, “Sunaye uku ne zuwa yanzu, tabbas sauran za su biyo baya.”
Tun bayan ɗarewarsa kan mulki a 2023, Tinubu bai naɗa jakadu ba har yanzu.
Mutane da dama sun daɗe suna ƙorafin kan jinkirin naɗa jakadun.
Amma wasu na ganin aike sunayen jakadun na da alaƙa da barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na ɗaukar matakin soji a kan Najeriya, kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.
A wata hira da aka yi da shi a watan Satumba, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce babu wata matsala game da jinkirin.
Ya ce, “Dukkanin ofisoshin jakadancinmu suna aiki yadda ya kamata. Kowace ofishi yana gudanar da ayyukansa yadda ya dace. Rashin jakadu ba zai haifar da giɓi ba.”
Ya ƙara da cewa duk da cewa jakada shi ne shugaban ofishin jakadanci, akwai kwamishinoni, wakilai da ma’aikatan diflomasiyya da ke tafiyar da harkokin yau da kullum.
A cewarsa, “Diflomasiyya ba aikin mutum ɗaya ba ne. Tsarin ya tanadi irin wannan yanayi.”
Tuggar, ya kuma ce shugaban ƙasa ne kaɗai ke da ikon naɗa jakadu, kuma zai yi hakan a lokacin da ya dace.
Ya bayyana cewa, “Shugaban ƙasa yana duba batun, kuma za a sanar da sunayen a lokacin da ya dace.”
Ya ƙara da cewa, “’Yan Najeriya a ƙasashen waje har yanzu suna samun ayyuka, kuma mu’amala da ƙasashen da muke hulɗa da su ba ta ragu ba.”
Ya ce kuma akwai ƙasashe da dama da suka shafe dogon lokaci ba tare da jakadu ba, amma hakan bai lalata dangantakarsu da wasu ƙasashe ba.
Ya ce, “Wannan ba sabon abu ba ne. Diflomasiyya tana da tanadin irin wannan yanayi. Abin da ya fi muhimmanci shi ne aiki, ba kwaikwayo ba.”
A ƙarshe ya ce Najeriya tana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran ƙasashen duniya.
“Manufofin ƙasashen waje na Najeriya sun bayyana, kuma ana jinmu a duniya. Abin da muke yi shi ne tabbatar da cewa ofisoshinmu suna samar da sakamako mai amfani ga ’yan Najeriya.”