HausaTv:
2025-06-28@11:17:35 GMT

Limamin Tehran:  Duniya Ce Ta Yi Yaki Da Iran

Published: 28th, June 2025 GMT

Wanda ya jagoranci sallar juma’a a Tehran ya bayyana cewa; A cikin kwanaki 12 da su ka gabata duniya ce ta yi yaki da Iran.

Hujjatul Islam Wal Muslimin   Abu Turabi Fard, ya fara hudubarsa da mika sakon ta’aziyyar shigowar ranakun Ashura, haka nan kuma jinjina ga shahidan jamhuriyar musulunci masu daraja da HKI ta yi wa kisan ta’addanci a tsawon kwanaki12 na yaki.

Limamin na Tehran ya kuma ce; Abubuwan da su ka faru a cikin kwanaki 12 na yaki sun bude wani sabon shafi na siyasa a cikin wannan yankin da kuma a fagen siyasar kasa da kasa.

Hari la yau limamin na Tehran ya jinjinawa jagoran juyin musulunci na Iran saboda yadda Iran a karkashin jagorancinsa ta zama cibiyar gwgawarmayar musulunci a cikin wannan yankin.

Limamin juma’ar na Tehran ya kuma kara da cewa; HKI ta kawo wa Iran hari ne a jajiberin ranar Idan Gadir bisa cikakken taimakon bayanai na asiri daga Amurka.”

Limamin ya kuma kara da cewa; Masu bin diddigin abubuwan da suke faruwa suna bayyana cewa; Makiya, sun dauki shekaru kusan 20 suna shirya wannan yakin. Shi kanshi fira ministan HKI ya yi furuci da hakan.

Hujjatul Islami Wal Muslimin Abu Turabi Fard ya kuma ce; HKI ta kawo wannan harin ne adaidai lokacin da ake tattaunawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a Tehran ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

Ya kuma bukaci al’ummar Musulmi da sauran al’ummar Kano da su yi amfani da wannan dama wajen yin tunani a kan ayyukan da suka yi a cikin shekarar da ta gabata, tare da yin addu’o’in zaman lafiya da hadin kai da ci gaba a jihar da kasa baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
  • An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
  • Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
  • Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani