Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@08:31:45 GMT

Likitoci Sun Shawarci Jama’a Su Rika Zuwa Asibiti Akai-Akai

Published: 14th, March 2025 GMT

Likitoci Sun Shawarci Jama’a Su Rika Zuwa Asibiti Akai-Akai

Babban magatakarda, sashin Nephrology, Federal Teaching Hospital Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga ya bukaci jama’a da su rungumi salon rayuwa mai inganci domin hana kamuwa da cutar koda.

 

Ya bayyana haka ne ga manema labarai a Gombe a yayin bikin ranar ciwon koda ta duniya.

 

Dokta Fidelis Linga ya bayyana halaye marasa kyau kamar yawan shan barasa, shan taba, cin abinci mara kyau, da kuma salon rayuwa a matsayin abubuwan da ke haifar da hauhawar cututtukan da ke da alaƙa da koda.

 

Ya kuma jaddada mahimmancin ziyarar asibitoci akai akai, da daidaita tsarin abinci, da motsa jiki a kai a kai wajen hana kamuwa da cutar koda.

 

Ya bayyana cewa a duniya baki daya, mutane miliyan 850 ne ke fama da cutar koda wanda miliyan 11 daga ciki ke mutuwa daga cutar a duk shekara yana mai bayyana yanayin a matsayin abin damuwa.

 

Dokta Fidelis Linga ya ce FTH Gombe na kokarin samar da karin injinan wankin koda wato dialysis da ma’aikatan lafiya don biyan bukatun dimbin masu cutar koda da ke zuwa wurin aikin wankin.

 

Ya ce an yi ƙoƙarin ne don inganta hanyar yin amfani da dialysis na ceton rai ga majinyata da ke fama da cututtukan koda.

 

HUDU Shehu/Gombe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

An rufe taron ministocin Sin da Afirka mai tabbatar da ci gaban hadin gwiwar da aka samu a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka wato FOCAC, wanda aka gudanar daga ranekun 10 zuwa 12 a birnin Changsha na lardin Hunan, matakin da ya bayar da sabbin damammaki ga kasashen Afirka, bisa shirin “manyan ayyuka 10 na abota tsakanin Sin da Afirka”. Sa’an nan, bayan an kammala taron, nan take, an kaddamar da bikin baje kolin kayayyaki hajojin Sin da Afirka karo na 4, duk a birnin Changsha, matakin da ya zamo daya daga cikin jerin ayyukan da ake gudanar da su don aiwatar da shirin “manyan ayyuka 10”, inda aka baje kolin ci gaban da aka samu, da tattara damammaki da albarkatu wuri guda, domin gaggauta samun ingantacciyar bunkasar hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren ciniki da tattalin arziki.

A cikin shekaru 25 da suka gabata, tun kafuwar FOCAC a shekarar 2000, yawan kudin kayayyakin da ake shigarwa da na fitarwa tsakanin Sin da Afirka ya karu zuwa dalar Amurka biliyan 292.4 a shekarar 2024 daga dalar biliyan 13.9 a 2000, inda adadin ya karu da fiye da ninki 20. Kana a cikin wasikar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika don taya murnar cimma nasarar gudanar da taron ministoci na wannan karo, Xi ya sanar da shirin yafe harajin kwastam na kaso 100% a kan kayayyakin kasashen Afirka 53, wadanda suka kulla dangantakar diflomasiyya da Sin, matakin da zai kara saukaka wa kasashen Afirka a fannin fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin.

Kazalika, a farkon watanni 5 na bana, yawan kudin da Sin ta kashe wajen shigo da kayayyakin Afrika zuwa cikin kasarta ya kai dalar Amurka biliyan 50.6, adadin da ya karu da kashi 1.6% bisa na makamancin lokacin bara. Hakan ya ba kasashen Afirka damar more babbar kasuwar Sin.

Hadin gwiwar Sin da Afirka na kara habaka, duba da yadda ake aiwatar da hakikanan matakai don tabbatar da manyan tsare-tsare da aka cimma, tare da mai da hankali matuka kan amfanar da al’ummun Afirka, da inganta karfin kasashen Afirka na samun bunkasuwa bisa dogaro da kai. Ma iya cewa, hadin gwiwar bangarorin Afirka da Sin ta fuskar ciniki da tattalin arizki na cikin wani yanayi mai armashi da dorewa, duk da kalubaloli, da sauye-sauyen yanayin da ake fuskanta a duniya, abin da sa ake samun cikakken kwarin gwiwa bisa hadin gwiwar kasashe masu tasowa da bunkasar duniya baki daya. (Mai zane da rubutu:MINA)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato