Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-30@21:50:18 GMT

Likitoci Sun Shawarci Jama’a Su Rika Zuwa Asibiti Akai-Akai

Published: 14th, March 2025 GMT

Likitoci Sun Shawarci Jama’a Su Rika Zuwa Asibiti Akai-Akai

Babban magatakarda, sashin Nephrology, Federal Teaching Hospital Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga ya bukaci jama’a da su rungumi salon rayuwa mai inganci domin hana kamuwa da cutar koda.

 

Ya bayyana haka ne ga manema labarai a Gombe a yayin bikin ranar ciwon koda ta duniya.

 

Dokta Fidelis Linga ya bayyana halaye marasa kyau kamar yawan shan barasa, shan taba, cin abinci mara kyau, da kuma salon rayuwa a matsayin abubuwan da ke haifar da hauhawar cututtukan da ke da alaƙa da koda.

 

Ya kuma jaddada mahimmancin ziyarar asibitoci akai akai, da daidaita tsarin abinci, da motsa jiki a kai a kai wajen hana kamuwa da cutar koda.

 

Ya bayyana cewa a duniya baki daya, mutane miliyan 850 ne ke fama da cutar koda wanda miliyan 11 daga ciki ke mutuwa daga cutar a duk shekara yana mai bayyana yanayin a matsayin abin damuwa.

 

Dokta Fidelis Linga ya ce FTH Gombe na kokarin samar da karin injinan wankin koda wato dialysis da ma’aikatan lafiya don biyan bukatun dimbin masu cutar koda da ke zuwa wurin aikin wankin.

 

Ya ce an yi ƙoƙarin ne don inganta hanyar yin amfani da dialysis na ceton rai ga majinyata da ke fama da cututtukan koda.

 

HUDU Shehu/Gombe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

2. Asibitin Turai Yar’Adua

3. Asibitin Amadi Rimi

4. Asibitin Jibia

5. Asibitin Funtua

Zango, ya ce gwamnati na ƙoƙarin tabbatar da cewa duk wanda ke fama da cutar ya samu magani cikin sauƙi ba tare da biyan kuɗi ba.

Zazzabin taifod yana yaɗuwa ne musamman a lokacin damina, kuma yana da nasaba da amfani da ruwa mai datti da rashin tsafta.

Alamomin cutar sun haɗa da ciwon ciki, ciwon kai, da gajiyar jiki.

Gwamnati ta shawarci jama’a da su riƙa kula da tsafta da kuma hanzarta zuwa asibiti idan sun ga irin waɗannan alamomi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Arewa za ta kayar da Tinubu a zaɓen 2027 —Babachir
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya