Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-17@23:17:32 GMT

Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500

Published: 14th, March 2025 GMT

Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500

Ministan kasa a ma’aitar tsaro, Mohammed Bello Matawalle, ya ba magoya bayan jam’iyyar (APC) a jihar Zamfara gudumuwar kudi naira miliyan 500 domin a taimaka musu wajen gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

 

Mai ba da shawara na musamman kan harkokin siyasa Mattawalle, Alhaji Ibrahim Danmalikin Gidan Goga ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau.

 

A cewar Gidan-Goga, Ministan ya zabi bayar da kudi ne maimakon kayan abinci, saboda tuni wasu ‘yan siyasa a jihar suka raba wa magoya bayansu hatsi.

 

Ya kuma jaddada cewa tallafin kudi zai baiwa magoya bayan jam’iyyar APC damar siyan wasu muhimman abubuwan da ake bukata a cikin watan Ramadan.

 

“A wannan karon, maimakon ba wa jama’a hatsi iri-iri, Ministan ya yanke shawarar bayar da tsabar kudi saboda wasu ‘yan siyasa sun riga sun raba kayan abinci,” ya bayyana.

 

Ya ci gaba da cewa, tsohon Gwamna Sanata Abdul Aziz Yari ya bayar da gudummawar tireloli na hatsi iri-iri 496, wanda hakan ya sa Ministan ya kara wannan kokari da tallafin kudi.

 

Gidan-Goga ya bayyana cewa, mutane 200 daga kowace karamar hukuma 14 da ke Zamfara sun karbi ₦100,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 280.

 

“Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC 24 daga kananan hukumomi biyar na shiyyar Sanatan Zamfara ta Yamma sun karbi ₦250,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 30.”

 

“Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC 90 daga kananan hukumomin jihar Zamfara ta tsakiya da kuma ta Zamfara ta Arewa sun karbi ₦250,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 22.5.”

 

Sauran nau’ikan wadanda suka ci gajiyar kuma sun sami kudade a matsayin wani bangare na kunshin jin dadin Ramadan na Minista.

 

Gidan-Goga ya tabbatar da cewa sama da kashi 80 cikin 100 na wadanda aka yi niyya sun karbi kudadensu.

 

Ya lura cewa wadanda suka amfana daga Bakura, Gummi, Kaura-Namoda, Maradun, Shinkafi, da Talata-Mafara duk sun tattara kudadensu.

 

Sai dai kawo yanzu mutum 100 da suka ci gajiyar tallafin daga kananan hukumomin Tsafe, Zurmi, Bungudu, Bukkuyum, da Anka ne kowannensu ya karbi nashi kason, yayin da sauran wadanda suka ci gajiyar shirin za a biya su nan gaba kadan.

 

Ya kara da cewa har yanzu wadanda suka ci gajiyar tallafin daga karamar hukumar Birnin Magaji ba su samu kudadensu ba sakamakon tsaikon da aka samu wajen gabatar da jerin sunayen wadanda suka karba.

 

 

 

AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Matawalle Zamfara da suka ci gajiyar wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara