Wasu manyan ƴan siyasa daga jam’iyyun adawa sun hallara a Cibiyar Yar’Adua da ke Abuja a yau Laraba da rana don taron ƙaddamar da sabbin shugabannin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), a wani mataki na shiryawa zaɓen shekarar 2027. Taron ya samu halartar manyan fitattun ’yan takara da tsofaffin gwamnoni daga sassa daban-daban na ƙasa.

Cikin waɗanda suka halarta akwai Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP; Peter Obi na LP; tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai; da tsohon Ministan Sufuri kuma gwamnan Rivers, Rotimi Amaechi. Haka kuma, Solomon Dalung, Dino Melaye, Dele Momodu, Sanata Gabriel Suswam, da Sanata Ireti Kingibe sun samu halarta. Emeka Ihedioha da Air Marshal Sadique Abubakar (rtd.) suma sun bayyana.

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC Ana Sa Ran Samun Bunkasuwar Dangantakar Sin Da Kungiyar SADC

A yayin taron, an sanar da cewa haɗakar jam’iyyun adawa ta ɗauki jam’iyyar ADC a hukumance a matsayin dandalin siyasa da za ta yi amfani da shi don ƙalubalantar jam’iyyar APC a 2027. An bayyana tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, a matsayin shugaban riko na ƙasa. Ya fice daga jam’iyyar PDP domin jagorantar sabon tsarin siyasar.

An kuma nada tsohon gwamnan Osun kuma jigon APC, Rauf Aregbesola, a matsayin sakataren riko na ƙasa, alamar yiwuwar sauyin tunani da haɗewar ƙarfi daga jam’iyyu daban-daban. Ana sa ran David Mark da sauran shugabanni za su fara ƙaddamar da sabuwar tafiyar siyasar, yayin da taron ke ci gaba a lokacin haɗa wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar da ƙaddamar bincike a game da harin da dakarunta suka kai kan wata cibiyar intanet da ke yankin Gaza, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar ɗimbin fararen hula a jiya Litinin.

Hukumar kare lafiyar fararen hula ta Falasɗinu, ta ce wasu daga cikin makaman da Isra’ila ta harba a jiya Litinin sun faɗa kan kasuwar kwamfuta ta ‘Al-baqa’ da ke gaɓar teku da ke birnin Gaza, kuma a wannan cibiyar kaɗai mutane 24 ne suka rasa raukansu.

Ɗaya daga cikin masu magana da yawun rundunar sojin Isra’ila ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa, tabbatas sun kai hare-hare kan wurare da dama da dakarun Hamas ke fakewa don gudanar da ayyukansu a Gaza, to amma sun ɗauki dukkanin matakan da suka wajaba domin taƙaita illolin farmakin ga fararen hula.

Ahmed al-Nayrab, mai shekaru 26 a duniya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira da rayukansu a wannan farmaki, ya ce lokacin da aka kai harin, akwai ɗimbin mutane da suka haɗa da masu shan shayi da kuma waɗanda suka zo don samun sadarwar intanet.

Ahmed ya ci gaba da cewa, “abin da ya faru a wannan wuri ba ya da bambanci da kisan kiyashi”, yana mai cewa “a duk inda ka duba sassan gaɓoɓi ne da kuma gangar jikunan mutane ne, yayin da wasu daga cikin gawarwakin ke ci da wuta kana wasu ke kwance jina-jina’’.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu
  • David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  • Ganduje: Dalori ya kira taron Majalisar Gudanarwar Jam’iyyar APC