Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
Published: 29th, June 2025 GMT
Al’ummar Ƙaramar Hukumar Isa da ke Jihar Sakkwato, sun roƙi gwamnatin jihar da ta Tarayya da jami’an tsaro da su kai musu ɗauki kan barazanar da ƙasurgumin ɗan bindiga Bello Turji ke musu.
A farkon makon nan ne aka samu labarin cewa Bello Turji ya bai wa mazauna wasu yankuna a Isa wa’adin gina masa ƙaramin dam ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.
Har ila yau, ya umarce su da su bar garuruwansu, domin ba ya buƙatar ganinsu a wajen.
Wani mazaunin yankin, Wanzami Abubakar Isa, ya bayyana damuwarsa cewa suna zaune garuruwansu kamar baƙi.
“Abin takaici ne yadda ’yan bindiga ke ba mu umarni a garinmu na haihuwa. Muna roƙon gwamnati ta taimake mu.“
Shi ma Alhaji Abdullahi Isa ya ce, “Rayuwarmu ta shiga mawuyacin hali. Ba za mu iya ci gaba da rayuwa a haka ba.
“Ta yaya za mu bar gidajenmu saboda barazanar ɗan bindiga? Gwamnati ta yi wani abu cikin gaggawa.”
Wani mazaunin yankin, Bashar Ahmad, ya ce ba daidai ba ne a bar Turji yake cin karensa babu babbaka.
“Gwamnati ta kare mu, mu ma ’yan ƙasa ne kuma muna da ’yancin zama lafiya.”
Sai dai duk ƙoƙarin jin ta bakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Isa, Alhaji Sharifu Kamarawa, da mai bai wa gwamna shawara kan harkar tsaro, Ahmad Usman, bai yi nasara ba, domin ba su amsa kira ko saƙon da aka aike musu ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Yanzu haka, ko da yake Turji bai bayyana ranar da zai kai hari ba, akwai fargaba sosai a yankin.
Jama’a na ganin ya kamata gwamnati ta ɗauki mataki mai tsauri, maimakon ci gaba da yin sulhu da ’yan bindigar da ke addabar yankin gabashin Sakkwato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗauki gwamnati hari Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
Daga cikin wadanda shugaban kasar ta Nigeria ya yi wa afuwa da kawai Maryam Sanda ‘yar shekaru 37 wacce aka yankewa hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda samunta da kashe mijinta da wuka a 2017.
Mai Magana da yawun shugaban kasa Bayo Onangua ya saki bayanin afuwar da shugaban kasar ya yi, wacce kuma ta hadad a Faruka Lawan tsohon dan majalisa da aka samu da laifin cin hanci da rashawa a 2021.
Sai kuma Ken Saro-wiwa wanda dan fafutuka ne mai rajin kare muhalli a yankin Ogoni da aka zartarwa hukuncin kisa a 1995.
Har ila yau afuwar ta shugaba Tunibu ta shafi Manjo Janar Mamman Jiya Vatsa wanda aka zartarwa da hukuncin kisa a 1986 saboda juyin Mulki.
Haka nan kuma shugaba Tinibu ya yafewa Sir Herbert Macaly dan kishin kasa da ya yi fada da ‘yan mulkin mallaka. ‘Yan mulkin mallaka ne su ka yanke masa hukunci a 1913.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci