Rundunar Sarayar Kudus dake karkashin kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da kai wa matsugunin ‘yan share wuri zauna na Sydriot hari da makamai masu linzami da su ka yi sanadiyyar kashe da jikkata sojojin mamaya.

 Su kuwa kafafen watsa labarun HKI sun samar da cewa, an tsinkayo harba makamai masu linzami guda 3 daga Gaza zuwa Sydriot.

A gefe daya dakarun “Kassam” na kungiyar Hamas sun sanar da cewa sun kai wasu hare-haren da makamai masu linzami zuwa yankin Q20 a sansanin ‘yan share wuri zauna na ” Nir-Ishaq” da “Miftahim.

Bugu da kari dakarun na “Sarayal-Kuds’ sun sanar da kai wa tankar yaki samfurin Mirkava hari ta hanyar wata nakiya mai karfi akan hanyar Zannah,dake gabashin unguwar Shuja’iyyah a birnin Gaza.

Abinda ya biyo baya shi ne kai wani harin da “Sarayal-Kuds’ ta yi akan sojojin mamaya da suke cikin wani gida, ta hanyar amfani da makamin TBG. Da dama daga cikin sojojin mamayar sun halaka da kuma jikkata.

A ranar Talatar da ta gabata ma dai dakarun “Sarayal-Kuds” sun kai wasu hare-haren na hadin gwiwa da ‘ Kassam’ akan  cincirindon sojojin mamaya a arewacin Khan-Yunus.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Sarayal Kuds

এছাড়াও পড়ুন:

Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati

Masu fafutuka a kasar Togo sun sanar da cewa an kashe mutane 7 a yayin Zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati da aka yi a makon da ya shude, suna masu tuhumar  jami’an tsaro da yin amfani da karfin da ya wuce haddi.

Kamfanin dillancin labarun “Reuters” wanda ya nakalto ‘yan fafutukar na kasar Togo, suna cewa; Jami’an tsaro sun yi amfani da karfi mai ban tsoro akan masu Zanga-zangar.”

Kungiyoyin fararen hula da na masu kare hakkokin dan’adam  12 ne su ka fitar da sanarwar, su ka kuma kara da cewa; jami’an tsaron kasar sun yi amfani da kulake wajen dukan masu Zanga-zangar, haka nan kuma igiyoyi da suke daure su, kamar kuma yadda su ka sace da lalata dukiyar mutane.

Har ila yau kungiyoyin sun sanar da samun gawawwakin mutane 3 a ranar juma’ar da ta gabata, 2 daga cikinsu na kananan yara ne da aka jefa a cikin wani tafki a gabashin birnin Lome. Sai kuma gawawwaki 2 na wasu ‘yan’uwa a tafkin yankin Icodesio, shi ma a cikin birnin Lome. Sai a ranar Asabar ne aka sami cikon gawawwakin mutane 2  a yankin Niconakiboyi.

Bayanin da ya fito daga gwamnatin kasar a ranar Lahadi shi ne cewa, mutanen da aka samo gawawwakinsu sun nitse ne a cikin ruwa, tare da taya iyalan wadanda su ka rasa rayukan nasu alhinin rashin da su ka yi.

 Masu Zanga-zangar dai suna nuna kin amincewa da yin dandazon mukamkan gwamanti a hannun shugana kasar da kuma rashin Shata hanyar kawo karshen abinda suke ganin a matsayin kama-karya.

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta bayyana abinda yake faruwa da ‘murkushe ‘yan hamayya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos
  • Amurka Ta Dakatar Da Tura Makamai Zuwa Kasar Ukraine Saboda Kada A Sami Karancinsu A Gida
  • Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  •  Na’im Kassim: Mamaya Tana Da Ranar Da Za Ta Zo Karshe
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya