Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
Published: 29th, June 2025 GMT
Sojojin mamayar HKI suna ci gaba da kai hare-hare a yammacin kogin Jordan, inda a safiyar yau lahadi su ka kutsa cikin wani gida a garin Jenin,kamar kuma yadda ‘yan share wuri zauna su ka kutsa gidan wani bafalasdine a kudancin Nablus.
Rahotanni da suke fitowa daga Falasdinu suna cewa; an yi taho mu gama a tsakanin Falasdinawa da ‘yan mamaya a garin Tal a kudancin Nablus.
A sansanin ‘yan hijira na Jenin sojojin na mamaya sun tarwatsa wani gida na Bafalasdine wanda ya haddasa tashin hayaki da kuma jin kara mai tsanani a sassa mabanbanta na garin Jenin.
Haka nan kuma ‘yan mamayar sun yi amfani da motar Buldoza wajen rusa wasu gidaje a sansanin na Jenin.
A makon da ya shude ma dai ‘yan mamayar sun rusa wasu gidaje masu yawa na Falasdinawa a yammacin Kogin Jordan a karkashin shirinsu na rusa gidaje 95.
A garin Tubas da yake a wannan yankin Iyalai da dama sun yi hijira saboda kaucewa hare-haren da ‘yan share wuri zauna suke kai musu.
Tun bayan 7 ga watan Oktoba na 2023 Amurka take goyon bayan HKI a yi wa Falasdinawan Gaza, kisan kiyashi da kuma kwacewa Falasdinawan yammacin Kogin Jordan gidajensu da zummar korarsu daga yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Majaliar Dokokin Kasar Corsica Ta Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu Sannan Ta Ki Amincewa Da HKI
Majalisar dokokin tsibirin Corsica a yankin Mediterranean, wacce ta kasance jiha ce a kasar Faransa, ta amince da kasar Falasdinunu a matsayin cikakken kasa mai zaman kanta a MDD.
Tsirin dai tana neman samun yanci daga kasar faransa, ta amince da samuwar kasar Falasdinu da kuma yin watsi da HKI a matsayin yar mamaya.
Kissan kiyashi mai ban tsoro wanda HKI take yi a zirin Gaza ya tada hankalin mutane da dama a duniya kuma ya shara fagen amincwa da kasar Falasdinu mai zaman kanta.
Labarin ya kara da cewa Marie-Antoinette Maupertuis shugaban majalisar dokokin kasar ta Corsican ne ya gabatar da bukatar amincewa da kasar Falasdini a majalisar. Ya ce bisa wasu dokokin MDD kasar Falasdinu kasace mai zaman kanta.
Daga baya shugaban majalisar ya bayyana a shafinsa na Intaernet kan cewa tsibirin mai neman yenci daga kasar Faransa ta amince da kasar Falasdinu mai zaman kanta ta kuma yi allawadai da kissan da sojojin yahudawan Isra’ila suke yi a Gaza.