Aminiya:
2025-07-03@04:51:07 GMT

Hamas ta karɓi tayin tsagaita wuta a Gaza

Published: 3rd, July 2025 GMT

Ƙungiyar Hamas ta sanar da karɓar tayin tsagaita wuta a yaƙin Gaza kuma tuni ta soma nazarin sabuwar yarjejeniyar aka gabatar mata.

Hamas wadda ta nuna alamun samun masalaha ta bayyana cewa manufar yarjejeniyar ita ce kawo ƙarshen hare-hare Isra’ila da janye dakarunta daga yankin.

Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC

Ƙungiyar ta ce tana tuntuɓar abokan shawararta, sannan ta jinjina wa ƙoƙarin masu shiga tsakanin.

Shugaban Amurka ne ya gabatar da yarjejeniyar tsagaita wutar ta kwana 60, wadda ya ce tuni gwamnatin Isra’ila ta amince da ita.

To sai dai rahotonni na cewa da dama cikin ministoci masu ra’ayin riƙau ba su gamsu da ita ba, yayin da Firaminista Benjamin Netanyahu ya dage cewa yana son kawo ƙashen Hamas.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sabani Tsakanin Bin Gafir, Smotresh Da Zamir Kan Makomar Fursinonin Yahudawa A Gaza

Barazanar babban hafsan hafsoshin sojojin HKI na fadada yaki a Gaza don kubutar da fursinoni yahudawa da suke hannun falasdinawa ya jawo cece kuce tsakaninsa da bin gafir da kuma Smotresh,

Kakafen yada labaran Ebri ko HKI sun bayyana cewa  ministan kudi na HKI Betsal’il da kuma Smotresh ministan tsaron cikin gida na haramtacciyar kasar suna daga cikin wadanda suke adawa da ra’ayin babban hafsan sojojin mamayar Iyyal Zaamir wanda yake son gaggauta fadada yakin da yake jagoranta a Gaza don kubutar da fursinonin yahudawan da suke hannun kungiyar Hamas da sauran falasdinawa a gaza.

Smotresh da kuma Ben gafir suna ganin fadada yakin zai kasance hatsari ga rayuwar fursinonin.

Jaridar ‘Yadi’un-Ahrunut’ ta nakalto ministocin na fadar haka a taron ministocin haramtacciyar kasar kan cewa suna son fursinoni yahudawa su dawo da rayukansu ba gawaki ba. Don haka suna bukatar a san abinda za’a yi wand aba zai jefa rayukansu cikin harsari ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
  • Sabani Tsakanin Bin Gafir, Smotresh Da Zamir Kan Makomar Fursinonin Yahudawa A Gaza
  • Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka