Sojojin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake yi wasu sabbin kutse a yankunan Quneitra na kasar Siriya

Rahotonni sun bayyana cewa:  Da sanyin safiya ne sojojin mamayar Isra’ila suka kutsa cikin yankunan garin Saida da kuma kauyen Abu Mathra da ke yankin kudancin Quneitra na kasar Siriya. 

Wannan ya zo daidai da wani sintiri da sojojin mamayar Isra’ila da ke ci gaba da yi a kauyen Kodna da ke cikin karkarar Quneitra, ba tare da wata arangama ko gargadi daga mahukuntan Siriya ba.

Ana ci gaba da yin shiru a hukumance dangane da irin wadannan tsauraran matakan da gwamnatin mamayar Isra’ila ke yi a kan iyakar kasar da tuddan Golan na Siriya da ta mamaye, lamarin da ya sanya ayar tambaya na cikin gida da na kasa da kasa game da yanayin tsaro a yankunan.

Kungiyar kare hakkin bil adama ta kasar Siriya ta sanya ido kan yadda sojojin mamayar Isra’ila da suka hada da tankar yaki da mota mai sulke da kuma babbar mota dauke da sojoji kusan 30, inda suka kutsa cikin kauyen al-Samadaniyya al-Sharqiya da ke cikin yankin Quneitra. Sojojin mamayar Isra’ila sun binciki gidaje da dama kafin su janye zuwa sansanonin su, ba tare da samun rahoton kama mutane ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mamayar Isra ila kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Duk ana dora alhakin yadda lamarin cinikin Bayi ya bunkasa kan wani mutum dan asalin kasar Birtaniyya da ake kira da suna,John Hawkins. Hawkins  shi ne mutumin da ya kara daukaka, bunkasa,da zamanan har da lamarin cinikin Bayi”manufa anan yayi  gyare- gyare daga yadda Turawan kasar Fotugal suka fara da barinsa,ya yi masa kwaskwarima,zuwa lamarin kasuwanci mai daraja”.

Jiragen ruwa suna tasowa daga Kasar Birtaniya ko kuma Ingila  da Bindigogi, Madubi,da kuma Giya,Jiragen na zuwa wani wurin da ake kira da suna inda ake daukar Bayi a kai su  kasar ko kasashen da suka saye su, yanzu wurin ana kiransa da suna yankin Neja Delta inda daga can ne kuma za ‘a fara tafiya, har sai sun kai inda zasu sauka; ,daga can kuma sai ‘yan kasa tu tarbe su, inda zasu basu makamai da kuma abubuwan shaye- shaye, su kuma su basu Bayi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Suna Shakku Kan Tsagaita Bude Wuta Zai Dore Da Isra’ila
  • Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
  • Faransa Tace Za’a Maida Takunkuman Tattalin Arziki Kan Kasar Iran Idan Taki Yarda Da Yarjeniyar da Trump Yake
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
  • An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran
  • Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI A Lokacinda Mayakan Ansarallah Suka Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kasar
  • Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP