Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin zai gudanar da taron manema labarai a ranar Alhamis mai zuwa, da misalin karfe 10 na safe domin yin bayani kan shagulgulan al’adu da za a yi na bikin cika shekaru 80 da samun nasarar yakin turjiyar jama’ar kasar Sin kan zaluncin Japanawa da kuma yakin duniya na biyu.

Jami’ai daga ma’aikatar al’adu da yawon bude ido da na hukumar gidan rediyo da talabijin ta kasar, da mataimakin shugaban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG), da shugaban gidan adana kayan tarihi na yakin turjiyar jama’ar kasar Sin kan zaluncin Japanawa, za su halarci taron manema labarun.

Za su yi wa manema labarai karin haske kan wani baje koli mai taken tunawa da fitattun ayyukan al’adu da abubuwa masu nasaba da hakan, sannan za su amsa tambayoyi daga manema labarai. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban majalisar dokokin jama’ar kasar Mexico Sergio Carlos Gutiérrez, ya bayyana yayin da wakilin babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG ya zanta da shi a kwanakin baya cewa, tunanin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama da shugaba Xi Jinping ya gabatar ya burge shi matuka.

Ya ce, an gabatar da tunanin don tattauna yadda sassan kasa da kasa za su zauna tare, da taimakawa juna, da amincewa da bambance-bambance a fannonin tattalin arziki, da yawan mutane, da yankunan kasa a tsakanin kasashen duniya, da sa kaimi ga maida bambance-bambance su zama hanyar dinkewa da juna, da kuma samar da kyakkyawan yanayin zaman rayuwar al’ummun kasa da kasa. Kana yana fatan jama’ar kasashen duniya ciki har da ta Sin da ta Mexico, za su ji dadin zaman rayuwa mai inganci.

Ban da wannan kuma, Gutiérrez ya yi nuni da cewa, Sin da kasashen Latin Amurka sun taimakawa juna, da more fasahohin samun ci gaban juna, da sa kaimi ga samun zaman rayuwar jama’a mai inganci, kana bangarorin biyu sun yi kokarin samar da yanayin zaman rayuwa mai tsaro, da inganci ga jama’arsu.

Ya ce, bisa yanayin da ake ciki a duniya, zurfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, zai jagoranci Sin da kasashen Latin Amurka, ga bin hanyar samar da zaman rayuwa mai inganci ga al’umma. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce; Dokar Majalisar Shawarar Musulunci Ta Kasar Kan Hukumar IAEA Dole Ne Aiki Da Ita
  • Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  • Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Suna Shakku Kan Tsagaita Bude Wuta Zai Dore Da Isra’ila
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
  • An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin