Sabani Tsakanin Bin Gafir, Smotresh Da Zamir Kan Makomar Fursinonin Yahudawa A Gaza
Published: 1st, July 2025 GMT
Barazanar babban hafsan hafsoshin sojojin HKI na fadada yaki a Gaza don kubutar da fursinoni yahudawa da suke hannun falasdinawa ya jawo cece kuce tsakaninsa da bin gafir da kuma Smotresh,
Kakafen yada labaran Ebri ko HKI sun bayyana cewa ministan kudi na HKI Betsal’il da kuma Smotresh ministan tsaron cikin gida na haramtacciyar kasar suna daga cikin wadanda suke adawa da ra’ayin babban hafsan sojojin mamayar Iyyal Zaamir wanda yake son gaggauta fadada yakin da yake jagoranta a Gaza don kubutar da fursinonin yahudawan da suke hannun kungiyar Hamas da sauran falasdinawa a gaza.
Smotresh da kuma Ben gafir suna ganin fadada yakin zai kasance hatsari ga rayuwar fursinonin.
Jaridar ‘Yadi’un-Ahrunut’ ta nakalto ministocin na fadar haka a taron ministocin haramtacciyar kasar kan cewa suna son fursinoni yahudawa su dawo da rayukansu ba gawaki ba. Don haka suna bukatar a san abinda za’a yi wand aba zai jefa rayukansu cikin harsari ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran
Shugabannin Faransa, Jamus, da Biritaniya: Sun kuduri aniyar farfado da tattaunawa da Iran
Kasashen Faransa da Jamus da Birtaniya sun bayyana aniyarsu ta farfado da shawarwari da Iran da Amurka dangane da shirin makamashin nukiliyar Iran da nufin cimma cikakkiyar yarjejeniya mai dorewa.
A cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa, kasashen uku sun yi la’akari da Shirin kunna yarjejeniyar fahimtar juna. A baya dai Faransa da Birtaniya da Jamus sun sanar da cewa za su ci gaba da neman hanyar diflomasiyya don warware rikicin, amma Iran ta tabbatar da cewa ba ta son ci gaba da tattaunawa a halin yanzu idan dai har za a kakaba mata takunkumi.
A gefe guda kuma shugabannin kasashen Birtaniya da Faransa da Jamus sun yi maraba da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a zirin Gaza tare da yin alkawarin dawo da taimakon jin kai da zarar an amince da yarjejeniyar.
A cikin sanarwar da suka fitar, shugabannin sun jaddada cewa, sun amince da cewa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya ba da cikakken goyon baya ga shirin na Gaza, da saukaka aiwatar da shi, tare da sa ido kan matakai na gaba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Isra’ila ta ce yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta fara aiki October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci