Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
Published: 12th, June 2025 GMT
Majalisar Dattawan Nijeriya ta bayyana shirin kafa dokar da za ta mayar da rantsar da shugaban kasar a kwaryar majalisar, maimakon yadda ake yi a dandalin taro na Eagle da ke tsakiyar birnin Abuja.
DW ta ruwaito cewa ita dai Majalisar Dokokin Nijeriya ta 10 ta yi fice wajen dauko batutuwan da ke haifar da cece-kuce, kama daga yunkurin mayar da yin zabe ya zama dole da kuma hukunta duk wanda ya ci mutuncin taken Nijeriya sai kuma wannan batu na amfani da doka domin sauya tarihin da aka daura dambarsa tun a shekara ta 1999 da aka sake kafa dimokuradiyya a kasar.
Tun daga wannan lokaci kawo yanzu ana rantasar da shugaban kasar ne a dandalin taro na kasa na Eagle da ke birnin Abuja, wurin da ke bayar da dama ga dubban ’yan Nijeriya su cire kwarkwatar idanuwansu yayin rantsar da shugaban da suka zaba.
A yanzu Majalisar Dattawan na son canza wannan al’ada, har ma da gwama batun da sanya shugaban Nijeriya ya rinka jawabi ga ‘yan majalsar a duk ranar dimukurdiyya 12 ga watan Yuni.
Tuni wannan mataki ya janyo mayar da martani a Nijeriyar, musamman wadanda da su aka yi gwagwarmayar yanke cibiyar sake kafa dimokuradiyya a kasar.
Domin sauya batu na tarihi ga muhimmin al’amari muhimmi ne a Nijeriyar, musamman danganta shi da ranar 12 ga watan Yuni da aka soke zaben da ake dangata shi da mafi sahihanci.
Sabo dai akan ce tirken wawa, domin shekaru 26 kenan da sake kafa dimokuradiyya da ake rantsar da sabon shugaban Nijeriya a dandalin Eagle din da ke tsakiyar birnin duk bayan shekaru hudu.
Majalisar Dokokin Nijeriyar dai kan gwada ta ga martanin ’yan kasar a kan wasu al’amura, inda daga baya ta kan janye batun wanda shi ne damar da dimukurdiyya ta bai wa ’yan kasa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya kai ziyara Jihar Neja domin jajanta wa mutanen Mokwa da iftila’in ambaliyar ruwa ya shafa.
Zulum ya kuma bayar da tallafin Naira miliyan 300 domin taimaka wa waɗanda iftila’in ya shafa.
Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3Zulum, ya ce Gwamnatin Borno ta kawo wannan taimako ne don tallafabwa gwamnatin Neja wajen rage raɗaɗin ambaliyar da ta kashe mutane da lalata dukiyoyi.
Ya kuma buƙaci sauran gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi su haɗa kai don kare al’umma daga iftila’i da sauyin yanayi ke haddasawa.
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya nuna godiya bisa wannan ziyara da tallafi.
Ya ce ya yi matuƙar farin ciki da irin wannan kulawa da ƙauna da Gwamnatin Borno ta nuna wa al’ummarsa.
Bago, ya tabbatar da cewa za a yi amfani da tallafin cikin gaskiya da adalci, tare da ci gaba da faɗakar da jama’a su guji gina gidaje a kusa da bakin kogi.
Zulum, ya samu rakiyar Sanata Mohammed Tahir Monguno, wasu ‘yan Majalisar Wakilai, Injiniya Bukar Talba, Hon. Abduljadir Rahis da mataimakin kakakin Majalisar Dokokin Jihar Borno, Injiniya Abdullahi Askira.