HausaTv:
2025-07-26@17:02:04 GMT

Rasha Tana Kokarin Kara Samun Gindin Zama A Cikin Nahiyar Afirka

Published: 10th, June 2025 GMT

Fadar mulkin Rasha ” Kremlin” ta sanar da cewa; Kasar Rasha tana fadada fafagen yin aiki da kasashen Afirka da su ka hada da fagage masu muhimmanci na soja da tsaro.

Kakakin fadar ta “Kremlin” Dmitry Viskov da yake amsa tambaya akan tasirin shigar Rasha cikin nahiyar Afirka, ya ce; Sannu a hankali Rasha tana kara shiga cikin nahiyar ta Afirka’ sannan kuma ya yi ishara da azamar da Rashan ta yi na ganin wannan alakar ta bunkasa tare da mayar da hankali akan tattalin arziki da kuma zuba hannun jari.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane

Kwanan nan, darektar zartaswa ta hukumar kula da matsugunan dan Adam ta MDD, Anacláudia Rossbach, ta yi hira da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG, a hedkwatar hukumar kula da matsugunan dan Adam ta MDD dake Nairobi, babban birnin Kenya.

Yayin da aka ambato sakamakon da ya fi jawo hankali da Sin ta samu yayin kyautata kauyuka zuwa matsayin birane da garuruwa, Rossbach ta bayyana cewa, Sin ta cimma nasarar kawar da talauci ga mutane miliyan 800, da kuma tafiya a kan hanyar kyautata kauyuka zuwa birane da garuruwa, kuma wannan darasi ne da ya cancanci kasashen Afirka wadanda suke fuskantar kalubalen kyautata kauyuka zuwa birane su yi koyi da shi.

Ta ce, nan da shekaru 25 masu zuwa, mutane kusan miliayn 800 na kasashen Afirka da na Latin Amurka za su yi kaura zuwa birane, kuma kasashen Asiya da dama su ma suna fuskantar kalubalen fama da talauci. A cewarta, birane na da muhimmanci sosai wajen kawar da talauci, kuma ba ma kawai ya kamata a ba da wurin kwana ga mutane a cikin birane ba, har ma ya dace a ba su damammakin samun ilmi, da guraben ayyukan yi da sauransu, da kuma samun hidimomin kiwon lafiya don kiyaye koshin lafiyarsu, kana ta ce, wannan shi ne muhimmin abun da za mu ci gaba da gudanarwa da kuma tattaunawa a kai. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha Ta Sha Alwashin Mayar Wa Da Nato Martani Mai Tsanani Idan Ta Kai Ma Ta Hari
  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Iran Ta Cilla Tauraron Dan’adam Mai Suna Nahid-2 A Yau
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71
  • Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu