Aminiya:
2025-09-17@21:52:19 GMT

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas

Published: 12th, June 2025 GMT

Rashin wutar lantarki a Arewa maso Gabashin Najeriya ya tilasta wa jama’a da ’yan kasuwa zaman ɗari-ɗari da asarar dukiya, sakamakon aikin da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ƙasa (TCN), ke yi na aikin sabbin turakun wutar lantarki.

Rashin wutar, wanda ya fara daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Yuni, ya shafi layin wutar lantarki na Jos–Bauchi–Gombe mai ƙarfin 132kV.

An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato  Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai

A Jihar Adamawa, musamman a birnin Yola, jama’a na cikin matsanancin hali.

Hajiya Aisha Babangida daga Jimeta, ta ce rashin wutar ya tilasta masa soye dukkanin naman ragon sallarta domin babu wutar da za ta ajiye shi a firinji.

“Na fi son dafawa, amma dole na soya gaba ɗaya. Wannan matsala ta wuta ta zo ne a lokacin da ake buƙatar wutar,” in ji ta.

Kasuwanci da harkokin yau da kullum sun tsaya cak a wurare da dama.

Adamu Abubakar, mai sayar da lemun kwalba a kasuwar Jimeta, ya koka da cewa rashin sanyin ruwa ya rage masa yawan kwastomomi.

“Mutane na so ruwan sanyi, amma ba zan iya samun mai sanyi ba. Ina amfani da ƙanƙara ne yanzu don na ci gaba da kasuwancina,” in ji shi.

Muhammad Zaharaddeen, wani barber mai shagon aski a Bauchi, ya ce kasuwancinsa ya durƙushe sakamakon rashin wutar lantarki.

“Shagona na buƙatar wutar lantarki sosai. Ko da na kunna janareta, farashin mai ya tashi fiye da yadda mutane ke biya a baya,” in ji shi.

“Da ba don wani ɗan kasuwanci da nake yi a gefe ba, da ko abinci ba zan iya siya ba.”

A Jalingo, babban birnin Jihar Taraba, asibitoci da ƙananan ‘yan kasuwa na kokawa kan hauhawar kuɗin aiki.

Asibitin Federal Medical Centre ya koma amfani da janareta, wanda hakan ke sa wa ana biyan maƙudan kuɗaɗe wajen zuba man fetur.

“An daɗe da yanke wutarmu, yanzu da aka dawo mana da ita, sai kuma ga wannan matsalar. Duk manyan na’urorinmu suna amfani ne da dizal,” in ji Dokta Aisha Adamu Sani, daraktar asibitin.

Masu niƙa, masu walda da masu ɗinki a Jalingo sun dakatar da aiki.

Mallam Haruna Garba, wanda ke da injin niƙa, ya ce ya rufe shagonsa gaba ɗaya.

“Ba zan iya niƙa babu wutar lantarki ba. Man fetur ya yi tsada sosai. Na rufe kasuwancina na ɗan lokaci,” in ji shi.

A Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, al’umma na fama da ƙarancin ruwa da hauhawar farashin ruwan sanyi da kayan masarufi.

Musa Adamu, mai sayar da lemu, ya ce: “Babu wuta, babu sanyi. Dole na ɗan kara farashi, amma ya kamata jama’a su fahimtci rayuwar da ake ciki,” in ji shi.

Masu ƙananan sana’o’i irin su Yusuf Bukar, wani masassaƙa a Damaturu, na kashe dubban Naira kullum wajen siyan mai domin kammala ayyukansu.

“Idan wannan hali ya ci gaba, zan rasa kwastomomina. Na kashe Naira 10,000 a jiya kacal a kan mai,” in ji shi cikin baƙin ciki.

TCN ta bayyana cewa katse wutar na da matuƙar muhimmanci domin kammala gina sabbin turakun wuta masu ƙarfin 330kV domin inganta tsarin samar da wutar a yankin.

Kakakin TCN, Ndidi Mbah, ta ce turakun za su zama mafita daga yawan katsewar wuta a gaba.

“Da zarar an kammala aikin, za a iya amfani da layin Bauchi da Gombe. Jos ma za ta iya riƙa kai wa Bauchi wuta kai-tsaye,” in ji ta.

Sai dai masana sun ɗora alhakin matsalar kan rashin wata hanya da za ake samar wa Arewa maso Gabas wuta.

Wani tsohon ma’aikacin TCN da ya nemi a sakaya sunansa ya ce: “Idan layin Jos-Bauchi-Gombe ya faɗi, kowa zai tsunduma cikin duhu. Ya kamata a ce an gina wata hanya ta biyu tun da daɗewa.”

Wannan ba shi ne karon farko da yankin ke faɗawa cikin duhu ba.

A baya, wasu da ba a san ko su waye ba sun lalata turakun wuta da bam, wanda ya sa aka ɗauke wuta gaba ɗaya a Arewa maso Gabas.

Sai dai wannan katsewar wutar wata hujja ce ta gaggawar sake fasalin tsarin wutar lantarki a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Lantarki Rashin Wuta Taraba Turaku wutar lantarki rashin wutar

এছাড়াও পড়ুন:

Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro

 Babban sakataren majalisar koli ta tsaron jamhuriyar musulunci ta Iran Dr. Ali Larijani ya bayyana cewa; Za a bunkasa aiki tare a tsakanin Iran da Saudiyya a fagagen tattalin arziki da kuma tsaro.

Dr. Larijani ya bayyana hakan ne jim kadan bayan fitowar daga ganawar da ya yi da Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mu8hammad Bin Salman.

Bugu da kari Dr. Ali Larijani ya ce a yayin ganawarwa da Yarima mai jiran gado na Saudiyya Muhammad Bin Salman, sun tattauna hanyoyin bunkasa alakar kasashensu ta fuskoki mabanbanta, da kara girman wannan alakar ta fuskar tattalin arzki da tsaro fiye da yadda take a yanzu.”

Haka nan kuma ya ce, za a yi aiki domin kawar da dukkanin abubuwan da suke kawo cikas a kan hanyar bunkasa wannan alakokin.

Dr. Ali Larijani ya kuma ce,an yi shawara akan yadda kasashen yankin za su bunkasa alakarsu ta tsaro domin ganin an tabbatar da zaman lafiya.

Da aka tambaye shi akan ko an sami sauyi akan mahangar kasashen Larabawa bayan harin da HKI ta kai wa Qatar, Dr.Ali Larijani ya ce; Tabbas da akwai sauyi a cikin yadda kasashen larabawa suke Kallon abubuwan da suke faruwa, domin suna ganin cewa kasantuwar HKI a cikin wannan yankin yana hana zaman  lafiya.

Babban sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya ziyarci Saudiyya inda ya gana da ministan tsaronta da kuma Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar Kasuwanci Da HKI September 17, 2025  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza September 17, 2025 Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki