Za’ayi tattaunawa ta gaba tsakanin Iran da Amurka a ranar Lahadi a Oman
Published: 10th, June 2025 GMT
Iran ta ce za a gudanar da zagaye na gaba na tattaunawa da Amurka a ranar Lahadi mai zuwa a Muscat, babban birnin kasar Oman.
Kakakin ma’aikatar Esmail Baghai a wata sanarwa da ya fitar ya ce “An shirya zagaye na gaba na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka a ranar Lahadi mai zuwa a birnin Muscat.”
Tun a watan Afrilu, Tehran da Washington ke gudanar da shawarwarin kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
An yi shawarwari guda uku a tsakanin kasashen biyu a birnin Muscat, yayin da sauran biyun suka gudana a Rome, babban birnin kasar Italiya.
Tehran da Washington sun gudanar da wadannan zagaye biyar na shawarwarin a shiga tsakanin kasar Oman, kan batun maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar 2015, wadda Amurka ta fice daga cikinta a shekarar 2018.
Sai dai shawarwarin na fuskantar cikas sakamakon bukatar da Amurka ta yi na cewa Iran ta daina tace sinadarin Uranium a matsayin wani bangare na sabuwar yarjejeniyar.
Iran dai ta jaddada cewa, ba za ta yi watsi da hakkinta na inganta sinadarin Uranium ba, wanda yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT) ta tanada.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Ce: Rashin Dakatar Da Uranium Da Dage Takunkumi Sune Hanyar Warware Takaddamar Da Ita
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Inganta sinadarin Uranium da ɗage takunkumai na iya sa tattaunawar ta yi amfani
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta cewa: A bayyane yake cewa cimma yarjejeniyar da za ta tabbatar da zaman lafiya na dindindin na shirin makamashin nukiliyar Iran abu ne mai yiyuwa, kuma ana iya cimma shi cikin sauri.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya rubuta a shafinsa na Twitter game da sabon zagayen tattaunawa tsakanin Iran da Amurka da kuma matsayin Iran a kansu yana mai cewa: Shugaba Trump ya bayyana a lokacin da ya shiga fadar White House cewa ba lallai ne Iran ta mallaki makamin nukiliya ba, wannan matsayi ya yi daidai da akidar Iran ta nukiliya, kuma za a iya la’akari da shi a matsayin tushen yarjejeniyar da za a iya cimmawa.
Ya kara da cewa: A yayin da ake ci gaba da tattaunawa a ranar Lahadi, a bayyane yake cewa yarjejeniyar da za ta tabbatar da ci gaba da zaman lafiya a shirin nukiliyar Iran na kan hanya, kuma za a iya cimmawa cikin gaggawa.