Leadership News Hausa:
2025-06-13@08:54:39 GMT

Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas

Published: 12th, June 2025 GMT

Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas

A cewarsa, gobarar na iya kasancewa ta samo asali ne daga wani gini da ke bayan gidan man.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar na iya tashi ne daga tankunan mai da ke ƙasa, kafin ta bazu zuwa cikin gidan man gaba ɗaya.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta yi gaggawar killace wajen domin hana cunkoso da tabbatar da tsaron jama’a yayin aikin kashe gobarar.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobarar, Shakiru Amodu, ya tabbatar da cewa an samu nasarar kashe gobarar kafin ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.

Kafin ƙarfe 6 na yamma, jami’an agajin gaggawa sun shawo kan lamarin gaba ɗaya, tare da killace yankin da abin ya shafa domin kaucewa wata barazana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center

Gwamnatin jihar Kano ta kafa wani kwamitin da zai binciki musabbabin gobarar da ta tashi a kwanan nan a kasuwar wayoyin hannu ta Farm Center da ke jihar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ce dai gobara ta tashi a kasuwar wacce aka yi kiyasin ta kone shaguna sama da 300 tare da janyo wa ’yan kasuwa asarar miliyoyin Naira.

Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4 Kotu ta yi fatali da bukatar Akpabio, ta umarce shi ya biya Natasha N100,000

Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Umar Ibrahim ne ya rantsar da kwamitin a madadin Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf.

Kwamitin dai kasance karkashin jagorancin Kwamishinan Ayyuka na Musammanna jihar, Alhaji Umar Ibrahim kuma yana da wakilai daga hukumomin gwamnati da jami’an tsaro da ma manyan masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci.

An dai dora wa kwamitin alhakin gano ainihin abin da ya haddasa gobarar sannan ya gano yawan asarar da aka tafka da kuma bayar da shawarwarin kauce wa sake aukurar irin ta a nan gaba.

Sakataren gwamnatin dai ya hori kwamitin da yin aiki tukuru wajen ganin ya sauke nauyin da aka dora masa.

Ya kuma yi kira ga kungiyoyi da daidaikun jama’a masu hannu da shuni da su taimaka wa ’yan kasuwar da tallafi ta hanyar asusun da gwamnati ta tanada, yana mai ba da tabbacin cewa za a yi adalci wajen rabon tallafin da aka tara.

Ana sa ran kwamitin zai kammala aikinsa tare da mika rahotonsa cikin mako daya daga kaddamar da shi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 
  • Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
  • Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya
  • Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa ’yan kasuwar katako tallafin ibtila’in gobara