Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Published: 12th, June 2025 GMT
Haka kuma, ya zargi Matawalle da karɓar Naira miliyan 300 daga tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, don a sako ɗaliban, amma ya bai wa ‘yan bindiga miliyan 30 kacal.
APC ta ƙaryata wannan zargi.
Ta kuma bayyana cewa zargin Kaura yana shafar wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar kamar tsohon Gwamna Abdulaziz Yari, wanda yanzu ke wakiltar Zamfara ta Yamma a Majalisar Dattawa.
Jam’iyyar APC ta ƙalubalanci Kaura da ya kawo hujjoji kan wannan zargi da kuma wasu mutane da aka sace a jihar, kamar satar ɗalibai mata 270 daga makarantar Government Girls Secondary School da ke Jangebe a ranar 26 ga watan Fabrairun 2021, da kuma satar ɗaliban Kwalejin Noma da Kiwo da ke Bakura.
APC ta jaddada cewa gwamnatin Matawalle ta yi ƙoƙari wajen yaƙi da ‘yan bindiga da ceto al’ummomi da dama.
Ta bayyana yankuna kamar Gwaram, Kanoma, Kaya, Faru, Janbako, Lilo da Anka, a matsayin wuraren da aka gudanar da ayyukan tsaro da taimako.
Jam’iyyar ta kuma ce tana duba yiwuwar ɗaukar matakin shari’a kan gidan talabijin na Maibiredi TV da ya watsa hirar da ake ganin an shirya don ɓata sunan ministan.
Ta zargi PDP da ƙoƙarin karkatar da hankalin jama’a daga gazawarta ta hanyar yaɗa ƙarya da tayar da fitina don samun moriyar siyasa.
A ƙarshe, APC ta yi kira ga mambobinta da su zauna lafiya da bin doka, inda ta bayar da tabbacin cewa gaskiya za ta fito fili, kuma za a yi adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Matawalle Zamfara Zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta yi fatali da bukatar Akpabio, ta umarce shi ya biya Natasha N100,000
Kotun Daukaka Kara da ke Abuja ta yi fatali da bukatun Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio kan dakatacciyar Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, sannan ta ci shi tarar Naira 100,000.
Kotun, wacce ke karkashin jagorancin Mai Shari’a Hamman Barka dai ta yi watsi da bukatun ne kan karar da aka shigar ranar 21 ga watan Mayun 2025, bayan neman bukatar janye karar da aka daukaka.
Bukatun dai na kunshe ne a cikin wasu kararraki masu lamba CV/395/M1/2025 da kuma CV/395/M2/2025, wadanda aka shigar a ranakun uku da kuma 25 ga watan Mayun 2025, wanda a cikinsu aka ambaci sunan Akpabio a matsayin mai daukaka kara.
DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a ManguWadanda ake kara kuma su ne Sanata Natasha da Magatakardar Majalisar Dokoki ta Kasa da Majalisar Dattawa da shugaban kwmaitin da’a, ladabtarwa da korafe-korafen jama’a na majalisar, Sanata Neda Imasuem.
Tun farko dai a cikin karar, Akpabio ya nemi kotun da ta kara masa lokacin da zai iya kalubalantar hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke mai lamba FHC/ABJ/CS/384/2025, wanda ta yanke ranar 10 ga watan Maris 2025 bisa hujjar cewa akwai kura-kurai a cikinsa.
Sai dai da take yanke nata hukuncin, kotun ta ce ta amince da bukatar janye kararrakin guda biyu, kamar yadda mai kara ya bukata.
Sai dai ta ce ta ci mai karar tara Naira 100,000, wadanda za a ba wacce aka yi kara.