Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna
Published: 10th, June 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Amurka Ya Siffata Masu Zanga-Zanga A Los Angeles Da Dabbobi
Shugaban kasar ta Amurka wanda ya gabatar da jawabi a gaban sojojin kasar a sansanin ‘Fort Bragg’ dake Jahar North Carolina ya bayyana cewa; Jahar Los Angeles tana fuskantar mamaya daga makiya ‘yan kasashen waje.”
Har ila yau shugaban na Amurka ya ce; Ba za mu bari a rika kai wa jami’an tsaron gwamnatin tarayya hari ba, ba kuma za mu bari a mamaye wani gari daga cikin garuruwan Amurka ba.”
Shugaban kasar ta Amurka ya kuma ce; Abinda birnin Los Angeles yake fuskanta hari ne daga kowace kusurwa da ‘yan daba suke yi, kuma suna dauke da tutocin kasashen waje.”
Birnin Los Angeles yana fuskantar gangami da Zanga-zanga saboda nuna kin amincewa da Shirin korar ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba.
An sami sabani da rashin jituwa a tsakanin gwamnatin tarayya da kuma ta jaha akan matakin da ya kamata a dauka domin magance matsalar bakin hauren.
Gwamnan Jahar ta Califonia ya zargi shugaban kasar Donald Tump da kama-karya saboda aikewa da sojoji akan titunan birnin domin fuskantar masu gangamin da Zanga-zangar.