Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
Published: 27th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Nasarawa ya hori Kiristoci masu niyyar ziyarar su zama jakadu na gari tare dayin addu’ar zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba idan sun isa can.
Gwamna Abdullahi Sule ya bayyana haka a lokacin bankwana da masu ziyarar su 162 da zasu tashi zuwa Isra’ila.
Gwamnan ya jaddada muhimmancin da’a a yayin tafiyar tasu, inda ya bayyana cewa su dauka su Allah ya nufa da wannan ziyarar a bana.
Ya kuma tabbatar wa maziyartan jihar cewa gwamnatin jihar ta himmatu wajen kyautata rayuwarsu, tare da samar da matsuguni da abinci kyauta a tsawon tafiyarsu.
Sakataren zartarwa na hukumar jin dadin hukumar kula da masu ziyarar kiristoci ta jihar Nasarawa, Davide Ayiwa, wanda ya yabawa gwamnatin jihar kan gyaran ofishin hukumar ya kuma bukaci maziyartan da su ci gaba da gudanar da aikinsu.
Bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Dr. Emmanuel Akabe da alkalin alkalan jihar, Mai shari’a Aisha Bashir Aliyu, kwamishiniyar yada labarai da sauran kwamishinoni da sakataren gwamnatin jihar Labaran Shu’iabu Magaji babban akanta janar na jihar.
COV/Aliyu Muraki/Lafia
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.