Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Published: 10th, June 2025 GMT
A wani taron sauraron bayanai da aka gudanar a kwanan baya, ‘yar majalisar wakilan kasar Amurka Madeleine Dean ta yi wa ministan kasuwanci na kasar, Howard Lutnick tambayoyi game da yanayin ciniki da manufofin harajin kwastam na kasar, inda ta tono shirmen da ke cikin matakan haraji da Amurka ta dauka a kan kayayyakin da take shigarwa daga kasa da kasa.
A hakika, a yayin da tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen duniya ke kara dunkulewa baki daya, kasa da kasa su kan samu mabambantan fifiko a sana’o’i daban daban sakamakon bambancin albarkatun da suke da su, ko kuma bambancin ci gabansu, lamarin da ya sa suke yin musayar kayayyakin da suke da fifikonsu don tabbatar da bunkasa ta bai daya, hakan nan kuma sana’o’i daban daban na dogara ga juna. Kamar yadda sauran kasashen duniya suke, kasar Amurka ita kanta ta amfana da bunkasuwar tattalin arzikin duniya da kuma ciniki mai ‘yanci.
Duk da haka, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauki matakan haraji na barkatai a yunkurin daidaita matsalar da ya kira wai “gibin kudin ciniki”, matakin da ba haifar da munanan matsalolin haraji a fadin duniya kawai ya yi ba, har da daga farashin kayayyaki a cikin kasar kansa. Lallai Amurka tana fama da rashin lafiya, amma ta sa sauran kasashe shan magani. Hakan ba zai taimaka ga daidaita matsalolin da tsarin tattalin arzikin kasar ke haifarwa ba, sai ma kara tsunduma shi cikin mawuyacin yanayin tattalin arziki. (Mai Zane:Mustapha Bulama)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu
‘Yan majalisar dokokin Amurka sun gabatar da wani kudirin doka da ke ba da shawarar sake duba alakar Amurka da Afirka ta Kudu da kuma kakaba takunkumi a kan wasu jami’ai da suka ki amincewa da manufofin Amurka na ketare.
Kwamitin harkokin wajen Amurka ya kada kuri’a don aikewa da daftarin kudiri a kan yin nazarin dangantakar Amurka da Afirka ta Kudu” zuwa ga babban zauren majalisar wakilai, inda za a kada kuri’a a kansa.
Wannan matakin na bukatar amincewa daga majalisun wakilai da na dattawa kafin ya zama doka, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.
‘Yar majalisar wakilai Ronny Jackson ce ta gabatar da kudirin dokar a watan Afrilun da ya gabata. Tana zargin Afirka ta Kudu da zagon kasa ga muradun Amurka ta hanyar kulla alaka ta kut da kut da Rasha da China, da kuma nuna adawa ga Isra’ila, gami da kuma gurfanar da ita a gaban kotun kasa da kasa kan batun kisan gilla a a kan al’ummar Palasdinu.
Kudirin ya ba da shawarar yin cikakken nazari kan alakar kasashen biyu da kuma bayyana jami’an gwamnatin Afirka ta Kudu da shugabannin jam’iyyar ANC wadanda suka cancanci a kakaba musu takunkumi.