Leadership News Hausa:
2025-07-27@00:41:52 GMT

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

Published: 10th, June 2025 GMT

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

A wani taron sauraron bayanai da aka gudanar a kwanan baya, ‘yar majalisar wakilan kasar Amurka Madeleine Dean ta yi wa ministan kasuwanci na kasar, Howard Lutnick tambayoyi game da yanayin ciniki da manufofin harajin kwastam na kasar, inda ta tono shirmen da ke cikin matakan haraji da Amurka ta dauka a kan kayayyakin da take shigarwa daga kasa da kasa.

Kasancewar ayaba tana girma ne a sassa masu zafi, galibin yankunan kasar Amurka ba su dace da nomansu ba. Ko a jihohin Hawaii da Florida da sauran sassan kasar Amurka da suka fi zafi ma, yawan ayabar da ake samarwa ba zai iya biyan bukatun kasuwannin Amurka ba, sabo da wasu dalilai na yanayi da kasuwanci.

A hakika, a yayin da tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen duniya ke kara dunkulewa baki daya, kasa da kasa su kan samu mabambantan fifiko a sana’o’i daban daban sakamakon bambancin albarkatun da suke da su, ko kuma bambancin ci gabansu, lamarin da ya sa suke yin musayar kayayyakin da suke da fifikonsu don tabbatar da bunkasa ta bai daya, hakan nan kuma sana’o’i daban daban na dogara ga juna. Kamar yadda sauran kasashen duniya suke, kasar Amurka ita kanta ta amfana da bunkasuwar tattalin arzikin duniya da kuma ciniki mai ‘yanci.

Duk da haka, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauki matakan haraji na barkatai a yunkurin daidaita matsalar da ya kira wai “gibin kudin ciniki”, matakin da ba haifar da munanan matsalolin haraji a fadin duniya kawai ya yi ba, har da daga farashin kayayyaki a cikin kasar kansa. Lallai Amurka tana fama da rashin lafiya, amma ta sa sauran kasashe shan magani. Hakan ba zai taimaka ga daidaita matsalolin da tsarin tattalin arzikin kasar ke haifarwa ba, sai ma kara tsunduma shi cikin mawuyacin yanayin tattalin arziki. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu

‘Yan majalisar dokokin Amurka sun gabatar da wani kudirin doka da ke ba da shawarar sake duba alakar Amurka da Afirka ta Kudu da kuma kakaba takunkumi a kan  wasu jami’ai da suka ki amincewa da manufofin Amurka na ketare.

Kwamitin harkokin wajen Amurka ya kada kuri’a don aikewa da daftarin kudiri a kan yin nazarin dangantakar Amurka da Afirka ta Kudu” zuwa ga babban zauren majalisar wakilai, inda za a kada kuri’a a kansa.

Wannan matakin na bukatar amincewa daga majalisun wakilai da na dattawa kafin ya zama doka, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.

‘Yar majalisar wakilai Ronny Jackson ce ta gabatar da kudirin dokar a watan Afrilun da ya gabata. Tana zargin Afirka ta Kudu da zagon kasa ga muradun Amurka ta hanyar kulla alaka ta kut da kut da Rasha da China, da kuma nuna adawa ga Isra’ila, gami  da kuma gurfanar da ita a gaban kotun kasa da kasa kan batun kisan gilla a a kan al’ummar Palasdinu.

Kudirin ya ba da shawarar yin cikakken nazari kan alakar kasashen biyu da kuma bayyana jami’an gwamnatin Afirka ta Kudu da shugabannin jam’iyyar ANC wadanda suka cancanci a kakaba musu takunkumi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 3.5 Wajen Gina Shaguna A Farm Centre
  • Mutanen A Netherlands Suna Zaman Dirshen Saboda Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Yadda masu yi wa kasa hidima za su ci arzikin yankunan da suke aiki
  • Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji
  • Iran Ta Zargi Amurka Da HKI Da Wargaza Dokokin Kasa Da Kasa Da Kuma Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa